< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
برای سالار مغنیان بر یدوتون. مزمور آساف آواز من بسوی خداست و فریادمی کنم. آواز من بسوی خداست گوش خود را به من فرا خواهد گرفت.۱
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
در روز تنگی خود خداوند را طلب کردم. در شب، دست من دراز شده، بازکشیده نگشت و جان من تسلی نپذیرفت.۲
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
خدا را یاد می‌کنم و پریشان می‌شوم. تفکر می‌نمایم و روح من متحیر می‌گردد، سلاه.۳
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
چشمانم را بیدار می‌داشتی. بی‌تاب می‌شدم وسخن نمی توانستم گفت.۴
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
درباره ایام قدیم تفکرکرده‌ام. درباره سالهای زمانهای سلف.۵
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
سرودشبانه خود را بخاطر می‌آورم و در دل خود تفکرمی کنم و روح من تفتیش نموده است.۶
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
مگر خداتا به ابد ترک خواهد کرد و دیگر هرگز راضی نخواهد شد.۷
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
آیا رحمت او تا به ابد زایل شده است؟ و قول او باطل گردیده تا ابدالاباد؟۸
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
آیاخدا رافت را فراموش کرده؟ و رحمت های خودرا در غضب مسدود ساخته است؟ سلاه.۹
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
پس گفتم این ضعف من است. زهی سالهای دست راست حضرت اعلی!۱۰
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
کارهای خداوند را ذکرخواهم نمود زیرا کار عجیب تو را که از قدیم است به یاد خواهم آورد.۱۱
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
و در جمیع کارهای تو تامل خواهم کرد و در صنعتهای تو تفکرخواهم نمود.۱۲
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
‌ای خدا، طریق تو در قدوسیت است. کیست خدای بزرگ مثل خدا؟۱۳
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
تو خدایی هستی که کارهای عجیب می‌کنی و قوت خویش را بر قوم‌ها معروف گردانیده‌ای.۱۴
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
قوم خود را به بازوی خویش رهانیده‌ای یعنی بنی یعقوب وبنی یوسف را. سلاه.۱۵
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
آبها تو را دید، ای خداآبها تو را دیده، متزلزل شد. لجه‌ها نیز سخت مضطرب گردید.۱۶
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
ابرها آب بریخت و افلاک رعد بداد. تیرهای تو نیز به هر طرف روان گردید.۱۷
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
صدای رعد تو در گردباد بود و برقها ربع مسکون را روشن کرد. پس زمین مرتعش و متزلزل گردید.۱۸
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
طریق تو در دریاست و راههای تو درآبهای فراوان و آثار تو را نتوان دانست.۱۹
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
قوم خود را مثل گوسفندان راهنمایی نمودی، به‌دست موسی و هارون.۲۰

< Zabura 77 >