< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Azava dziesma, dziedātāju vadonim Jedutunam. Es saucu ar savu balsi uz Dievu un brēcu, es saucu uz Dievu, un Viņš klausās uz mani.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
Bēdu laikā es meklēju To Kungu, mana roka izstiepjas naktī un nenogurst, mana dvēsele negribās būt iepriecināma.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Kad es Dievu pieminu, tad es nopūšos; kad es apdomāju, tad mana sirds bēdājās. (Sela)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Tu turi nomodā manas acis es esmu tā izmisis, ka nespēju runāt.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Es pieminu vecos laikus, senos gadus,
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Es atminu savu dziesmu naktī, mana sirds ir domu pilna, mans gars meklē gaismu.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Vai tad Tas Kungs atstums mūžīgi un vairs nebūs žēlīgs?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Vai tad Viņa žēlastība mitēsies mūžam? Vai tā solīšana pagalam uz bērnu bērniem?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Vai tad Dievs ir aizmirsis žēlot? Vai Viņš aizslēdzis dusmībā Savu sirds žēlastību? (Sela)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Tad es saku: tās ir manas bēdas; tā Visuaugstākā labā roka to var nogriezt.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Es pieminu Tā Kunga darbus, es tiešām pieminu Tavus brīnumus no veciem laikiem.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Es pārdomāju visus Tavus darbus un pieminu, ko Tu dari.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Ak Dievs, Tavs ceļš ir svēts; kur ir tāds liels Dievs, kā Tu, Dievs?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Tu esi tas stiprais Dievs, kas brīnumus dara; Savu spēku Tu esi darījis zināmu tautu starpā.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Savus ļaudis Tu esi atpestījis ar stipru elkoni, Jēkaba un Jāzepa bērnus. (Sela)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Ūdeņi Tevi redzēja, ak Dievs! ūdeņi Tevi redzēja un drebēja, pat dziļumi trīcēja.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Biezie padebeši izgāza ūdeņus, augstie padebeši izlaida pērkonus, un Tavas bultas šaudījās.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
Tavi pērkoni rūca viesulī, zibeņi apspulgoja zemi, zeme trīcēja un drebēja.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Tavs ceļš bija jūrā un Tavs gājums dziļos ūdeņos, un Tavas pēdas nebija manāmas.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Tu vadīji Savus ļaudis kā avju pulku caur Mozu un Āronu.

< Zabura 77 >