< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
In finem, pro Idithun, Psalmus Asaph. Voce mea ad Dominum clamavi: voce mea ad Deum, et intendit mihi.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
In die tribulationis meæ Deum exquisivi, manibus meis nocte contra eum: et non sum deceptus. Renuit consolari anima mea,
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
memor fui Dei, et delectatus sum, et exercitatus sum: et defecit spiritus meus.
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Anticipaverunt vigilias oculi mei: turbatus sum, et non sum locutus.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Cogitavi dies antiquos: et annos æternos in mente habui.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Et meditatus sum nocte cum corde meo, et exercitabar, et scopebam spiritum meum.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Numquid in æternum proiiciet Deus: aut non apponet ut complacitior sit adhuc?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Aut in finem misericordiam suam abscindet, a generatione in generationem?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Aut obliviscetur misereri Deus? aut continebit in ira sua misericordias suas?
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Et dixi nunc cœpi: hæc mutatio dexteræ Excelsi.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Memor fui operum Domini: quia memor ero ab initio mirabilium tuorum,
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
et meditabor in omnibus operibus tuis: et in adinventionibus tuis exercebor.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Deus in sancto via tua: quis Deus magnus sicut Deus noster?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Tu es Deus qui facis mirabilia. Notam fecisti in populis virtutem tuam:
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
redemisti in brachio tuo populum tuum, filios Iacob, et Ioseph.
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Viderunt te aquæ Deus, viderunt te aquæ: et timuerunt, et turbatæ sunt abyssi.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Multitudo sonitus aquarum: vocem dederunt nubes. Etenim sagittæ tuæ transeunt:
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
vox tonitrui tui in rota. Illuxerunt coruscationes tuæ orbi terræ: commota est et contremuit terra.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
In mari via tua, et semitæ tuæ in aquis multis: et vestigia tua non cognoscentur.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Deduxisti sicut oves populum tuum, in manu Moysi et Aaron.

< Zabura 77 >