< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Pour la fin, pour Idithun, psaume d’Asaph. De ma voix j’ai crié au Seigneur; de ma voix j’ai crié à Dieu, et il m’a prêté attention.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
Au jour de ma tribulation j’ai recherché Dieu: mes mains durant la nuit, ont été étendues vers lui; et mon espérance n’a point été déçue.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Je me suis souvenu de Dieu, et j’ai été ravi de joie; je me suis exercé à méditer, et mon esprit a défailli.
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Mes yeux ont anticipé les veilles de la nuit; j’ai été troublé, et je n’ai point parlé.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
J’ai pensé aux jours anciens; et j’ai eu les années éternelles dans l’esprit.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Et j’ai médité la nuit avec mon cœur, je m’exerçais à prier et je sondais mon esprit.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Est-ce que Dieu nous rejettera éternellement? ou ne sera-t-il pas de nouveau plus favorable encore?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Ou retranchera-t-il sans fin sa miséricorde, de génération en génération?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Ou Dieu oubliera-t-il d’avoir pitié? ou contiendra-t-il, dans sa colère, ses miséricordes?
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Et j’ai dit: C’est maintenant que je commence; ce changement est l’ œuvre de la droite du Très-Haut.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Je me suis souvenu des œuvres du Seigneur, je me souviendrai aussi de vos merveilles depuis le commencement.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Je méditerai sur toutes vos œuvres, et je m’exercerai dans vos desseins.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Ô Dieu, votre voie est sainte: quel Dieu est grand comme notre Dieu?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Vous êtes le Dieu qui faites des merveilles. Vous avez fait connaître parmi les peuples votre puissance;
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Vous avez racheté par votre bras votre peuple, les fils de Jacob et de Joseph.
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Les eaux vous ont vu, ô Dieu, les eaux vous ont vu; et elles ont craint, et les abîmes ont été troublés.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Il y a eu un grand bruit des eaux: les nuées ont fait entendre leur voix.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
La voix de votre tonnerre a éclaté sur la roue.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Dans la mer a été votre route, et vos sentiers ont été de grandes eaux: et vos traces ne seront pas connues.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Vous avez conduit, comme des brebis, votre peuple par les mains de Moïse et d’Aaron.

< Zabura 77 >