< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Ma voix s'adresse à Dieu, et je crie, ma voix s'adresse à Dieu, et il m'écoutera.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
Au jour de ma détresse, j'ai cherché le Seigneur; la nuit, ma main était étendue vers lui et ne se lassait point; mon âme refusait d'être consolée.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Je me souvenais de Dieu, et je gémissais; je méditais, et mon esprit était abattu. (Sélah, pause)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Tu avais retenu mes yeux dans les veilles; j'étais troublé, je ne pouvais parler.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Je pensais aux jours d'autrefois, aux années des temps passés.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Je me rappelais mes mélodies de la nuit; je méditais en mon cœur, et mon esprit examinait.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Le Seigneur rejettera-t-il pour toujours, ne sera-t-il plus désormais propice?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Sa bonté a-t-elle cessé pour toujours? Sa parole a-t-elle pris fin pour tous les âges?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Dieu a-t-il oublié d'avoir pitié? A-t-il dans sa colère fermé ses compassions?
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Et j'ai dit: Voilà ce qui fait ma souffrance: C'est que la droite du Très-Haut a changé.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Je me rappellerai les exploits de l'Éternel, me souvenant de tes merveilles d'autrefois;
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Je méditerai sur toutes tes œuvres, et je considérerai tes hauts faits.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
O Dieu, tes voies sont saintes! Quel autre Dieu est grand comme Dieu?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Tu es le Dieu qui fait des merveilles; tu as fait connaître ta force parmi les peuples.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Par ton bras, tu rachetas ton peuple, les enfants de Jacob et de Joseph. (Sélah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Les eaux te virent, ô Dieu! Les eaux te virent; elles tremblèrent; même les abîmes s'émurent.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Les nues se répandirent en eaux; les nuages tonnèrent; tes traits aussi volèrent çà et là.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
Ton tonnerre gronda dans le tourbillon; les éclairs brillèrent sur le monde; la terre s'émut et trembla.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Tu as fait ton chemin dans la mer, tes sentiers dans les grandes eaux; et tes traces n'ont point été connues.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Tu as conduit ton peuple comme un troupeau, par la main de Moïse et d'Aaron.

< Zabura 77 >