< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Au maître de chant, ... Idithun. Psaume d’Asaph. Ma voix s’élève vers Dieu, et je crie; ma voix s’élève vers Dieu: qu’il m’entende!
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
Au jour de ma détresse, je cherche le Seigneur; mes mains sont étendues la nuit sans se lasser; mon âme refuse toute consolation.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Je me souviens de Dieu, et je gémis; je médite, et mon esprit est abattu. — Séla.
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Tu tiens mes paupières ouvertes; et, dans mon agitation, je ne puis parler.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Alors je pense aux jours anciens, aux années d’autrefois.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Je me rappelle mes cantiques pendant la nuit, je réfléchis au dedans de mon cœur, et mon esprit se demande:
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
« Le Seigneur rejettera-t-il pour toujours, ne sera-t-il plus favorable?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Sa bonté est-elle épuisée pour jamais, en est-ce fait de ses promesses pour les âges futurs?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Dieu a-t-il oublié sa clémence, a-t-il, dans sa colère, retiré sa miséricorde? » — Séla.
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Je dis: « Ce qui fait ma souffrance, c’est que la droite du Très-Haut a changé! »
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Je veux rappeler les œuvres de Yahweh, car je me souviens de tes merveilles d’autrefois,
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Je veux réfléchir sur toutes tes œuvres, et méditer sur tes hauts faits.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
O Dieu, tes voies sont saintes: quel Dieu est grand comme notre Dieu?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Tu es le Dieu qui fait des prodiges; tu as manifesté ta puissance parmi les nations.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Par ton bras, tu as délivré ton peuple, les fils de Jacob et de Joseph. — Séla.
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Les eaux t’ont vu, ô Dieu, les eaux t’ont vu, et elles ont tremblé; les abîmes se sont émus.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Les nuées déversèrent leurs eaux, les nues firent entendre leur voix, et tes flèches volèrent de toutes parts.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
Ton tonnerre retentit dans le tourbillon; les éclairs illuminèrent le monde; la terre frémit et trembla.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
La mer fut ton chemin, les grandes eaux ton sentier, et l’on ne put reconnaître tes traces.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Tu as conduit ton peuple comme un troupeau, par la main de Moïse et d’Aaron.

< Zabura 77 >