< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
I CRIED unto God with my voice, even unto God with my voice; and he gave ear unto me.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
In the day of my trouble I sought the Lord: my sore ran in the night, and ceased not: my soul refused to be comforted.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
I remembered God, and was troubled: I complained, and my spirit was overwhelmed. (Selah)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Thou holdest mine eyes waking: I am so troubled that I cannot speak.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
I have considered the days of old, the years of ancient times.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
I call to remembrance my song in the night: I commune with mine own heart: and my spirit made diligent search.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Will the Lord cast off for ever? and will he be favourable no more?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Is his mercy clean gone for ever? doth his promise fail for evermore?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Hath God forgotten to be gracious? hath he in anger shut up his tender mercies? (Selah)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
And I said, This is my infirmity: but I will remember the years of the right hand of the most High.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
I will remember the works of the Lord: surely I will remember thy wonders of old.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
I will meditate also of all thy work, and talk of thy doings.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Thy way, O God, is in the sanctuary: who is so great a God as our God?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Thou art the God that doest wonders: thou hast declared thy strength among the people.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Thou hast with thine arm redeemed thy people, the sons of Jacob and Joseph. (Selah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
The waters saw thee, O God, the waters saw thee; they were afraid: the depths also were troubled.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
The clouds poured out water: the skies sent out a sound: thine arrows also went abroad.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
The voice of thy thunder was in the heaven: the lightnings lightened the world: the earth trembled and shook.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Thy way is in the sea, and thy path in the great waters, and thy footsteps are not known.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Thou leddest thy people like a flock by the hand of Moses and Aaron.

< Zabura 77 >