< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
For the excellent musician Ieduthun. A Psalme committed to Asaph. My voyce came to God, when I cryed: my voyce came to God, and he heard me.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
In the day of my trouble I sought ye Lord: my sore ranne and ceased not in the night: my soule refused comfort.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
I did thinke vpon God, and was troubled: I praied, and my spirit was full of anguish. (Selah)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Thou keepest mine eyes waking: I was astonied and could not speake.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Then I considered the daies of olde, and the yeeres of ancient time.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
I called to remembrance my song in the night: I communed with mine owne heart, and my spirit searched diligently.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Will the Lord absent him selfe for euer? and will he shewe no more fauour?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Is his mercie cleane gone for euer? doeth his promise faile for euermore?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Hath God forgotten to be mercifull? hath he shut vp his teder mercies in displeasure? (Selah)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
And I sayde, This is my death: yet I remembred the yeeres of the right hand of the most High.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
I remembred the workes of the Lord: certainely I remembred thy wonders of olde.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
I did also meditate all thy woorkes, and did deuise of thine actes, saying,
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Thy way, O God, is in the Sanctuarie: who is so great a God as our God!
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Thou art ye God that doest wonders: thou hast declared thy power among the people.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Thou hast redeemed thy people with thine arme, euen the sonnes of Iaakob and Ioseph. (Selah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
The waters sawe thee, O God: the waters sawe thee, and were afraide: yea, the depths trembled.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
The cloudes powred out water: the heauens gaue a sounde: yea, thine arrowes went abroade.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
The voyce of thy thunder was rounde about: the lightnings lightened the worlde: the earth trembled and shooke.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Thy way is in the Sea, and thy paths in the great waters, and thy footesteps are not knowen.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Thou diddest leade thy people like sheepe by the hand of Moses and Aaron.

< Zabura 77 >