< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Unto the end, for Idithun, a psalm of Asaph. I cried to the Lord with my voice; to God with my voice, and he gave ear to me.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
In the day of my trouble I sought God, with my hands lifted up to him in the night, and I was not deceived. My soul refused to be comforted:
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
I remembered God, and was delighted, and was exercised, and my spirit swooned away.
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
My eyes prevented the watches: I was troubled, and I spoke not.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
I thought upon the days of old: and I had in my mind the eternal years.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
And I meditated in the night with my own heart: and I was exercised and I swept my spirit.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Will God then cast off for ever? or will he never be more favourable again?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Or will he cut off his mercy for ever, from generation to generation?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Or will God forget to shew mercy? or will he in his anger shut up his mercies?
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
And I said, Now have I begun: this is the change of the right hand of the most High.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
I remembered the works of the Lord: for I will be mindful of thy wonders from the beginning.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
And I will meditate on all thy works: and will be employed in thy inventions.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Thy way, O God, is in the holy place: who is the great God like our God?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Thou art the God that dost wonders. Thou hast made thy power known among the nations:
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
With thy arm thou hast redeemed thy people the children of Jacob and of Joseph.
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
The waters saw thee, O God, the waters saw thee: and they were afraid, and the depths were troubled.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Great was the noise of the waters: the clouds sent out a sound. For thy arrows pass:
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
The voice of thy thunder in a wheel. Thy lightnings enlightened the world: the earth shook and trembled.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Thy way is in the sea, and thy paths in many waters: and thy footsteps shall not be known.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Thou hast conducted thy people like sheep, by the hand of Moses and Aaron.

< Zabura 77 >