< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
A ti, ó Deus, glorificamos, a ti damos louvor, pois o teu nome está perto, as tuas maravilhas o declaram.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
Quando eu occupar o logar determinado, julgarei rectamente.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
A terra e todos os seus moradores estão dissolvidos, mas eu fortaleci as suas columnas (Selah)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
Disse eu aos loucos: Não enlouqueçaes; e aos impios: Não levanteis a fronte:
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Não levanteis a vossa fronte altiva, nem falleis com cerviz dura;
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Porque nem do oriente, nem do occidente, nem do deserto vem a exaltação.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
Mas Deus é o Juiz; a um abate, e a outro exalta.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
Porque na mão do Senhor ha um calix, cujo vinho é roxo; está cheio de mistura; e dá a beber d'elle; mas as fezes d'elle todos os impios da terra as sorverão e beberão.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
E eu o declararei para sempre; cantarei louvores ao Deus de Jacob.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
E quebrarei todas as forças dos impios, mas as forças dos justos serão exaltadas.