< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
Siyakubonga, Nkulunkulu, siyabonga, ukuthi ibizo lakho liseduze, iyalandisa imisebenzi yakho emangalisayo.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
Lapho ngisemukela isikhathi esimisiweyo ngizakwahlulela ngokuqonda.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
Umhlaba labo bonke abakhileyo kuwo kuncibilikile; mina ngiqinisa insika zawo. (Sela)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
Ngathi kwabayiziwula: Lingabi yiziwula. Lakwababi: Lingaphakamisi uphondo.
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Lingaphakamiseli phezulu uphondo lwenu, lingakhulumi ngentamo elukhuni.
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Ngoba ukuphakanyiswa kakuveli empumalanga kumbe entshonalanga njalo hatshi enkangala.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
Kodwa uNkulunkulu ungumahluleli, uyehlisa omunye, aphakamise omunye.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
Ngoba esandleni seNkosi kulenkezo; lewayini liphuphuma, ligcwele inhlanganiso; iyathulula okwalo; kodwa izibhidi zalo, ababi bonke bomhlaba bazazihluza bazinathe.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Kodwa mina ngizatshumayela njalonjalo, ngihlabele indumiso kuNkulunkulu kaJakobe.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
Njalo zonke impondo zababi ngizaziquma; impondo zabalungileyo zizaphakanyiswa.