< Zabura 75 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
In finem, ne corrumpas. Psalmus cantici Asaph. [Confitebimur tibi, Deus, confitebimur, et invocabimus nomen tuum; narrabimus mirabilia tua.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
Cum accepero tempus, ego justitias judicabo.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
Liquefacta est terra et omnes qui habitant in ea: ego confirmavi columnas ejus.
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
Dixi iniquis: Nolite inique agere: et delinquentibus: Nolite exaltare cornu:
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
nolite extollere in altum cornu vestrum; nolite loqui adversus Deum iniquitatem.
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Quia neque ab oriente, neque ab occidente, neque a desertis montibus:
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
quoniam Deus judex est. Hunc humiliat, et hunc exaltat:
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
quia calix in manu Domini vini meri, plenus misto. Et inclinavit ex hoc in hoc; verumtamen fæx ejus non est exinanita: bibent omnes peccatores terræ.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Ego autem annuntiabo in sæculum; cantabo Deo Jacob:
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
et omnia cornua peccatorum confringam, et exaltabuntur cornua justi.]

< Zabura 75 >