< Zabura 75 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
Per il Capo de’ musici. “Non distruggere”. Salmo di Asaf. Canto. Noi ti celebriamo, o Dio, ti celebriamo; quelli che invocano il tuo nome narrano le tue maraviglie.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
Quando verrà il tempo che avrò fissato, io giudicherò dirittamente.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
Si dissolva la terra con tutti i suoi abitanti, io ne rendo stabili le colonne. (Sela)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
Io dico agli orgogliosi: Non vi gloriate! e agli empi: non alzate il corno!
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Non levate il vostro corno in alto, non parlate col collo duro!
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Poiché non è dal levante né dal ponente, né dal mezzogiorno che vien l’elevazione;
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
ma Dio è quel che giudica; egli abbassa l’uno ed innalza l’altro.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
L’Eterno ha in mano una coppa, ove spumeggia un vino pien di mistura. Egli ne mesce; certo, tutti gli empi della terra ne succeranno e berranno le fecce.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Ma io proclamerò del continuo queste cose, salmeggerò all’Iddio di Giacobbe;
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
spezzerò tutta la potenza degli empi, ma la potenza de’ giusti sarà accresciuta.

< Zabura 75 >