< Zabura 75 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
Dem Vorsänger, “Verdirb nicht!” Ein Psalm von Asaph, ein Lied. Wir preisen dich, o Gott, wir preisen dich; und nahe ist dein Name, deine Wundertaten verkündigen es.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
“Wenn ich die Versammlung empfangen werde, will ich in Geradheit richten.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
Zerschmolzen sind die Erde und alle ihre Bewohner: Ich habe ihre Säulen festgestellt.” (Sela)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
Ich sprach zu den Übermütigen: Seid nicht übermütig! und zu den Gesetzlosen: Erhebet nicht das Horn!
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Erhebet nicht hoch euer Horn; redet nicht Freches mit gerecktem Halse!
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Denn nicht von Osten, noch von Westen, und nicht von Süden her kommt Erhöhung.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
Denn Gott ist Richter; diesen erniedrigt er, und jenen erhöht er.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
Denn ein Becher ist in der Hand Jehovas, und er schäumt von Wein, ist voll von Würzwein, und er schenkt daraus: ja, seine Hefen müssen schlürfend trinken alle Gesetzlosen der Erde.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Ich aber, ich will es verkünden ewiglich, will Psalmen singen dem Gott Jakobs.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
Und alle Hörner der Gesetzlosen werde ich abhauen; es werden erhöht werden die Hörner der Gerechten.

< Zabura 75 >