< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
Nous te louons, ô Dieu, nous te louons, et ton nom est près de nous; on raconte tes merveilles.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
Au terme que j'ai fixé, je jugerai avec droiture.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
La terre tremblait avec tous ses habitants; moi j'ai affermi ses colonnes. (Sélah)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
J'ai dit aux superbes: Ne faites pas les superbes; et aux méchants: Ne levez pas la corne;
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Ne levez pas votre corne en haut; ne raidissez pas le cou pour parler avec insolence!
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Car ce n'est pas de l'orient, ni de l'occident, ni du désert que vient l'élévation;
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
Car c'est Dieu qui juge; il abaisse l'un et élève l'autre.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
Car il y a dans la main de l'Éternel une coupe où le vin bouillonne; elle est pleine de vin mêlé, et il en verse; certes, tous les méchants de la terre en boiront les lies.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Et moi, je le raconterai à jamais; je chanterai au Dieu de Jacob.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
Je romprai toutes les forces des méchants; mais les forces du juste seront élevées.