< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
Jusqu'à la Fin. Ne détruis pas; psaume et cantique d'Asaph, Nous te rendrons grâces, ô Dieu, nous te rendrons grâces, et nous invoquerons ton nom. Je raconterai toutes tes merveilles.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
Quand j'aurai pris mon temps, je jugerai avec droiture.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
La terre s'est liquéfiée avec tous ceux qui l'habitent, et moi j'ai raffermi ses colonnes.
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
J'ai dit aux pervers: Gardez-vous de faire le mal; et aux pécheurs: Ne levez pas le front.
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Ne levez pas le front avec orgueil; ne parlez pas injustement contre Dieu.
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Car le secours ne viendra ni de l'Orient, ni du Couchant, ni des montagnes du désert.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
Car Dieu seul est le juge: il humilie celui-ci, il exalte celui-là.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
Il y a dans la main du Seigneur un calice plein de vin sans mélange. Il l'incline çà et là, mais jamais il ne l'épuise jusqu'à la lie; tous les pécheurs de la terre en boiront.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Pour moi, je tressaillirai d'une allégresse perpétuelle; je chanterai au Dieu de Jacob.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
Et je briserai le front de tous les pécheurs, et le front des justes sera exalté.