< Zabura 75 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
For the chief musician; set to Al Tashheth. A psalm of Asaph, a song. We give thanks to you, God; we give thanks, for you reveal your presence; people tell of your wondrous works.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
At the appointed time I will judge fairly.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
Though the earth and all the inhabitants shake in fear, I make steady the earth's pillars. (Selah)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
I said to the arrogant, “Do not be arrogant,” and to the wicked, “Do not lift up the horn.
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Do not lift up your horn to the heights; do not speak with an insolent neck.”
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
It is not from the east or from the west, and it is not from the wilderness that lifting up comes.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
But God is the judge; he brings down and he lifts up.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
For Yahweh holds in his hand a cup of foaming wine, which is mixed with spices, and pours it out. Surely all the wicked of the earth will drink it to the last drop.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
But I will continually tell what you have done; I will sing praises to the God of Jacob.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
He says, “I will cut off all the horns of the wicked, but the horns of the righteous will be raised up.”

< Zabura 75 >