< Zabura 75 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
We give thanks to you; our God, we thank you. You are close to us, and we proclaim to others the wonderful things that you have done [for us].
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
[You have said], “I have appointed a time when I will judge people, and I will judge [everyone] fairly.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
When the earth shakes and all the creatures on the earth tremble, I am the one who will (keep its foundations steady/prevent it from being destroyed).
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
I say to people who (boast/talk proudly about themselves), ‘Stop bragging!’ and I say to wicked people, ‘Do not proudly [do things to] show how great you are [IDM]!
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Do not be arrogant, and do not speak so boastfully!’”
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
The one who judges people does not come from the east or from the west, and he does not come from the desert.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
God is the one who judges people; he says that some have sinned and must be punished, and that others have not done what is wrong.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
[It is as though] Yahweh holds a cup in his hand; it is filled with wine that [has spices] mixed in it [to cause those who drink it to become more drunk]; and when Yahweh pours it out, he will force all the wicked people to drink it; they will drink every drop of it, [which means that he will give them all the punishment that they deserve].
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
But [as for me], I will never stop saying what the God whom Jacob [worshiped has done]; I will never quit singing to praise him.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
He will destroy the power [IDM] of wicked people, but he will cause righteous people to become more powerful.

< Zabura 75 >