< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
Unto the end. May you not be corrupted. A Canticle Psalm of Asaph. We will confess to you, O God. We will confess, and we will call upon your name. We will describe your wonders.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
While I have time, I will judge justices.
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
The earth has been dissolved, with all who dwell in it. I have confirmed its pillars.
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
I said to the iniquitous: “Do not act unjustly,” and to the offenders: “Do not exalt the horn.”
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
Do not exalt your horn on high. Do not speak iniquity against God.
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
For it is neither from the east, nor from the west, nor before the desert mountains.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
For God is judge. This one he humbles and that one he exalts.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
For, in the hand of the Lord, there is a cup of undiluted wine, full of consternation. And he has tipped it from here to there. So, truly, its dregs have not been emptied. All the sinners of the earth will drink.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
But I will announce it in every age. I will sing to the God of Jacob.
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
And I will break all the horns of sinners. And the horns of the just will be exalted.