< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
(Til Sangmesteren. Al-tasjhet. En Salme af Asaf. En sang.) Vi takker dig, Gud, vi takker dig; de, der påkalder dit Navn, fortæller dine Undere.
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
"Selv om jeg udsætter Sagen, dømmer jeg dog med Retfærd;
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
vakler end Jorden og alle, som bor derpå, har jeg dog grundfæstet dens Støtter." (Sela)
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
Til Dårerne siger jeg: "Vær ej Dårer!" og til de gudløse: "Løft ej Hornet,
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
løft ikke eders Horn mod Himlen, tal ikke med knejsende Nakke!"
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
Thi hverken fra Øst eller Vest kommer Hjælp, ej heller fra Ørk eller Bjerge.
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
Nej, den, som dømmer, er Gud, han nedbøjer en, ophøjer en anden.
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
Thi i HERRENs Hånd er et Bæger med skummende, krydet Vin. han skænker i for een efter een, selv Bærmen drikker de ud; alle Jordens gudløse drikker.
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
Men jeg skal juble evindelig, lovsynge Jakobs Gud;
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
alle de gudløses Horn stødes af, de retfærdiges Horn skal knejse!