< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Maskil de Asaf. ¿Por qué, oh Dios, nos desechas para siempre? ¿Por qué arde tu ira contra el rebaño de tu dehesa?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Acuérdate de tu grey que hiciste tuya desde antiguo, de la estirpe que rescataste para hacerla tu herencia; del monte Sión que elegiste para morada tuya.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Dirige tus pasos hacia esas perpetuas ruinas: todo lo ha devastado el enemigo en el Santuario.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Los que te odian rugieron en el recinto de tus asambleas; pusieron sus enseñas por trofeo.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Talaron allí como quien alza la segur en lo espeso de la selva;
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
y ya con hacha y martillo hacen pedazos sus puertas.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Entregaron al fuego tu Santuario, profanaron, arrasándolo, el tabernáculo de tu Nombre.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
Decían en su corazón: “Destruyámoslos por completo; pegad fuego a todas las sinagogas de Dios en el país.”
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Ya no vemos nuestras señales, ya no hay profeta, ni queda entre nosotros quien sepa hasta cuándo.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
¿Hasta cuándo, oh Dios, nos afrentará el enemigo? ¿Ha de blasfemar siempre tu Nombre el adversario?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
¿Por qué retiras tu mano y retienes en tu seno tu diestra?
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Porque Tú, Yahvé, eres nuestro Rey, el que de antiguo ha obrado la salvación en medio de la tierra.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Tú dividiste el mar con tu poder y quebrantaste la cabeza de los dragones en las aguas;
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Tú aplastaste las cabezas de Leviatán, y lo diste por comida a las fieras que pueblan el desierto.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Tú hiciste brotar fuentes y torrentes, y secaste ríos perennes.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Tuyo es el día y tuya la noche; Tú pusiste los astros y el sol.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Tú trazaste todos los confines de la tierra; el verano y el invierno Tú los hiciste.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Recuérdalo Yahvé: el enemigo blasfema; un pueblo impío ultraja tu Nombre.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
No entregues al buitre la vida de tu tórtola; no quieras olvidar perpetuamente a tus pobres.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Vuelve los ojos a tu alianza, pues todos los rincones del país son guaridas de violencia;
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
no sea que el oprimido, en su confusión, se vuelva atrás; puedan el pobre y el desvalido alabar tu Nombre.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Levántate, Dios, defiende tu causa; recuerda cómo el insensato te insulta continuamente.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
No te olvides del vocerío de tus adversarios, porque crece el tumulto de los que se levantan contra Ti.

< Zabura 74 >