< Zabura 74 >
1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Pesem ukovita, Asafu. Zakaj, Bog, zametaš vekomaj, vedno kadí se jeza tvoja v čedo paše tvoje!
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Spomni se občine svoje; da si prej pridobil, odkupil rod posesti svoje, da je to gora Sijonska, na kateri si prebival.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Vzdigni noge svoje na večne podrtije, na vse zlo, kar ga dela sovražnik v svetem kraji.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Rujoveč so sovražniki tvoji sredi zbirališč tvojih postavili znamenja svoja, za znamenja.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Za plemenitega so imeli izmed njih vsakega, kakor je dvigal kvišku nad zapleteno lesovje sekire.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
Še zdaj bijejo izdolbene podobe njegove vkup s kolom in s kladivi.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Zažgali so svetišča tvoja, pahnili so na tla in oskrunili prebivališče tvojega imena.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
Rekli so v srci svojem: Zgrabimo ga vsi vkup; zapalili so vsa zbirališča Boga mogočnega, in pahnili jih na tla.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Znamenj naših ne vidimo, ni več preroka, in ni ga pri nas, ki bi vedel, doklej.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Doklej, o Bog, bode zasramoval sovražnik, dražil bode neprijatelj ime tvoje vekomaj?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Zakaj odtezaš roko svojo, in desnico svojo? Iz srede nedrija svojega strahúj.
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Saj Bog je kralj moj že od nekdaj, delajoč blaginjo sredi zemlje.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Ti si razklal v moči svoji morje; razbil si zmajem glave v vodah.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Ti si razbil somu glave, dajal si hrane samemu ljudstvu, potujočemu skozi puščavo.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Ti si odprl studenec in potok; ti posušaš reke mogočne.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Tvoj je dan, in tvoja noč; ti si napravil luč njeno in solnce.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Ti si postavil vse meje zemlji; samo poletje in zimo napravil si tí.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Spomni se vendar tega, da sovražnik zasramuje, o Gospod, in da ljudstvo nespametno draži ime tvoje.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Ne dajaj tistemu krdelu življenja grlice svoje, krdela ubozih svojih ne pozabi vekomaj.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Ozri se na zavezo, ker napolnjeni so najskrivnejši kraji zemlje, silovitosti so jama.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Kdor je ponižan, naj se ne vrne zmeden; ubogi in potrebni naj hvalita ime tvoje.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Vstani, o Bog; potegni se za pravdo svojo; spomni se zasramovanja svojega, katero ti dela nespametni vsak dan.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Ne pozabi glasú sovražnikov svojih; ropota spenjajočih se v té, ki se množi vedno.