< Zabura 74 >
1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Oh Bog, zakaj nas zavračaš za vedno? Zakaj se tvoja jeza kadi proti ovcam tvoje paše?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Spomni se svoje skupnosti, ki si jo odkupil od davnine, palico svoje dediščine, ki si jo odkupil, to goro Sion, kjer prebivaš.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Dvigni svoja stopala k neprestanim opustošenjem, celó vsemu kar je sovražnik zlobnega storil v svetišču.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Tvoji sovražniki rjovijo v sredi tvojih skupnosti, svoje zastave so postavili za znamenja.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Človek je bil slaven, če je nad debela drevesa dvigoval sekire.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
Toda sedaj so s sekirami in kladivi takoj zlomili rezljano delo le-tega.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Ogenj so vrgli v tvoje svetišče, s podrtjem do tal so omadeževali bivališče tvojega imena.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
V svojih srcih so rekli: »Skupaj jih uničimo.« V deželi so požgali vse Božje sinagoge.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Ne vidimo svojih znamenj. Nobenega preroka ni več niti tukaj med nami ni nobenega, ki ve doklej.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Oh Bog, doklej bo nasprotnik grajal? Mar bo sovražnik na veke preklinjal tvoje ime?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Zakaj umikaš svojo roko, celó svojo desnico? Iztrgaj jo iz svojega naročja.
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Kajti Bog je moj Kralj od davnine, ki dela rešitev duš v sredi zemlje.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
S svojo močjo si razdelil morje. Razbijaš glave zmajem v vodah.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Razbijaš glave leviatána na koščke in ga daješ, da postane hrana ljudstvu, ki prebiva v divjini.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Združil si studenec in morje, osušuješ mogočne reke.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Dan je tvoj, tudi noč je tvoja, pripravil si svetlobo in sonce.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Določil si vse meje zemlje. Naredil si poletje in zimo.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Spomni se, da je sovražnik grajal, oh Gospod in da je nespametno ljudstvo izrekalo bogokletje proti tvojemu imenu.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Oh ne izročaj duše svoje grlice množici zlobnih. Ne pozabi skupnosti svojih ubogih na veke.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Ozri se k zavezi, kajti temni kraji zemlje so polni prebivališč krutosti.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Oh naj se zatirani ne vrne osramočen. Naj ubog in pomoči potreben hvalita tvoje ime.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Vstani, oh Bog, zagovarjaj svojo lastno pravdo. Spomni se, kako te nespameten človek dnevno graja.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Ne pozabi glasu svojih sovražnikov. Hrup teh, ki vstajajo zoper tebe, se nenehno povečuje.