< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Instrução de Asafe: Deus, por que nos rejeitaste para sempre? [Por que] tua ira fumega contra as ovelhas do teu pasto?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Lembra-te do teu povo, que tu compraste desde a antiguidade; a tribo de tua herança, que resgataste; o monte Sião, em que habitaste.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Percorre as ruínas duradouras, tudo que o inimigo destruiu no santuário.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Os teus inimigos rugiram no meio de tuas assembleias; puseram por sinais de vitória os símbolos deles.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Eles eram como o que levantam machados contra os troncos das árvores.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
E agora, com machados e martelos, quebraram todas as obras entalhadas.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Puseram fogo no teu santuário; profanaram [levando] ao chão o lugar onde o teu nome habita.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
Disseram em seus corações: Nós os destruiremos por completo; serão queimadas todas as assembleias de Deus na terra.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Já não vemos os nossos sinais; já não há mais profeta; e ninguém entre nós sabe até quando será assim.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Deus, até quando o adversário insultará? O inimigo blasfemará o teu nome para sempre?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Por que está afastada a tua mão direita? Tira-a do teu peito!
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Deus é o meu Rei desde a antiguidade; ele opera salvação no meio da terra.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Tu dividiste o mar com a tua força; quebraste as cabeças dos monstros nas águas.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Despedaçaste as cabeças do leviatã; e o deste como alimento ao povo do deserto.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Tu dividiste a fonte e o ribeiro; tu secaste os rios perenes.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
A ti pertence o dia, a noite também é tua; tu preparaste a luz e o sol.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Tu estabeleceste todos os limites da terra; tu formaste o verão e o inverno.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Lembra-te disto: que o inimigo insultou ao SENHOR; e um povo tolo blasfemou o teu nome.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Não entregues a vida da tua pombinha para os animais selvagens; não te esqueças para sempre da vida dos teus pobres.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Olha para o [teu] pacto, porque os lugares escuros da terra estão cheios de habitações violentas.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Não permitas que o oprimido volte humilhado; que o aflito e o necessitado louvem o teu nome.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Levanta-te, Deus; luta em favor de tua causa; lembra-te do insulto que o tolo faz a ti o dia todo.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Não te esqueças da voz dos teus adversários; o barulho dos que se levantam contra ti sobe cada vez mais.

< Zabura 74 >