< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
En læresalme av Asaf. Hvorfor, Gud, har du forkastet oss for evig tid? Hvorfor ryker din vrede mot den hjord du før?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Kom i hu din menighet, som du vant din i fordums tid, som du gjenløste til å være din arvs stamme, Sions berg, hvor du tok bolig!
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Opløft dine trin til de evige grushoper! Alt har fienden fordervet i helligdommen.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Dine motstandere har brølt midt i ditt forsamlingshus; de har satt sine egne tegn op til tegn.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Det var et syn som når økser løftes i tykke skogen.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
Og nu, alt det som fantes av billedverk, det slo de sønder med øks og hammer.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
De har satt ild på din helligdom; like til grunnen har de vanhelliget ditt navns bolig.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
De har sagt i sitt hjerte: Vi vil ødelegge dem alle tilsammen! De har opbrent alle Guds forsamlingshus i landet.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Våre egne tegn ser vi ikke; det er ikke nogen profet mere, ikke nogen hos oss som vet hvor lenge det skal vare.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Hvor lenge, Gud, skal motstanderen håne, fienden forakte ditt navn evindelig?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Hvorfor drar du din hånd, din høire hånd tilbake? Ta den ut av din barm og ødelegg!
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Gud er dog min konge fra fordums tid, han som skaper frelse på den vide jord.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Du er den som skilte havet med din styrke, knuste dragenes hoder på vannene.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Du sønderslo Leviatans hoder, du gav den til føde for ørkenens folk.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Du lot kilde og bekk bryte frem, du uttørket evige strømmer.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Dig hører dagen til, dig også natten; du har skapt himmellysene og solen.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Du har fastsatt alle jordens grenser; sommer og vinter - du har dannet dem.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Kom dette i hu: Fienden har hånet Herren, og et dårlig folk har foraktet ditt navn!
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Overgi ikke din turteldue til den mordlystne skare, glem ikke dine elendiges skare evindelig!
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Se til pakten! For landets mørke steder er fulle av volds boliger.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
La ikke den undertrykte vende tilbake med skam, la den elendige og fattige love ditt navn!
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Reis dig, Gud, før din sak, kom i hu at du blir hånet av dåren hele dagen!
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Glem ikke dine fienders røst, dine motstanderes bulder, som stiger op all tid!

< Zabura 74 >