< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Ry Andrianañahare, ino ty ifaria’o anay zafe-anake? Ino ty ifomboa’o o añondry fiandraze’oo?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Tiahio i valobohòke vinili’o haehaey, i foko jineba’o ho lova’oy! naho ty vohi’ i Tsiône fimoneña’oy.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Aonjono o fandia’oo mb’amy hakoahañe nainai’ey, jinoi’ i rafelahiy ze hene raha an-toe’ i miavakey ao.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Niroharoha añivo’ o famantaña’oo o rafelahi’oo; najado’ iareo ty vilo’ iareo ho viloñe.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Sata’e ty maonjom-pekoñe añ’ala matahetse ao;
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
Ie henaneo, mamatsike am-pekoñe naho rabosàke o varamba’e nitsenèñe an-tsokitseo.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Finorototo’ iereo pak’an-tane i efe’o miavakey; nitivae’ iereo i fimoneñan- tahina’o masiñey.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
Hoe ty fisafirin-tro’iareo: Antao haharo ambaneñe iaby iereo; Fonga nitomontoe’ iareo o toem-pivorin’ Añahare an-taneo.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Tsy mahatrea o vilo’aio zahay; tsy amam-pitoky ka; naho tsy ama’ay ty mahafohiñe te hombia.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Pak’ombia ry Andrianañahare, te mbe hanìtse avao i rafelahiy? Ho tsambolitio’ o malaiñ’azo nainai’e hao i tahina’oy?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Ino ty nanitaha’o ty fità’o? I fitàn-kavana’oy? Afaho boak’ añ’araña’o ao ty fità’o, vaho mongoro?
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Toe mpanjakako boake haehae t’i Andrianañahare, mitoloñe fandrombahañe an-tane atoy.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Riniaria’o an-kaozarañe i riakey vaho dinemo’o an-drano ao o loha’ i fañaneñeio.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Hinoto’o o loha’ i fañanen-driakeio, hamahana’o o mpimoneñe am-patrañeo.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Nipoñafe’o o rano mitsiritsiokeo naho o sakao; nimaihe’o o oñe mikararake nainai’eo.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Azo ty antoandro, Azo ka ty haleñe; fa nihajarie’o o hazavàñeo naho i àndroy
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Najado’o iaby o fiefe­tsefe’ ty tane toio, nanoe’o ty asotry naho ty asara.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Tiahio, ry Iehovà, te niteratera i rafelahiy, vaho nitivae’ o lo-tsere­keo i Tahina’oy.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Ko atolo’o ami’ty biby hàko ty deho’o, ko haliño’o nainai’e o nanilofe’oo.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Ambeno i fañinay, fa atseke kibohon-kasiahañe o toetse maieñe’ an-taneo!
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Ko hampolie’o an-kasalarañe o demokeo! fa hibango i tahina’oy o misotrio naho o poie’eo.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Miongaha, ry Andrianañahare, ihalalio o azoo; tiahio ty fiterà’ i dagolay lomoñandro.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Ko haliño ty feo’ o rafelahi’oo; mitoabotse nainai’e ty fifandragaragà’ o mitroatse ama’oo.

< Zabura 74 >