< Zabura 74 >
1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Maskîl d’Assaph. Pourquoi, ô Dieu, nous délaisses-tu obstinément, ta colère est-elle embrasée contre le troupeau de ton pacage?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Souviens-toi de ta communauté, que tu acquis jadis, de ta tribu, ta propriété, que tu délivras, de ce mont Sion où tu fixas ta résidence!
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Dirige tes pas vers ces ruines irréparables: l’ennemi a tout dévasté dans le sanctuaire.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Tes adversaires ont poussé des rugissements dans l’enceinte de ton lieu de rendez-vous; là, ils ont imposé leurs emblèmes comme emblèmes.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
Ils y ont paru comme des gens qui brandissent la hache en plein fourré;
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
et puis, à coups de marteaux et de cognées, ils en ont abattu toutes les sculptures à la fois.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Ils ont livré aux flammes ton sanctuaire, jeté à bas et profané la résidence de ton nom.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
Ils ont dit en leur cœur: "Nous allons les dompter tous!" Ils ont brûlé tous les centres consacrés à Dieu dans le pays.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Nous ne voyons plus nos emblèmes à nous; plus de prophètes! plus personne avec nous, qui sache combien de temps cela durera!
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Jusqu’à quand, ô Dieu, l’adversaire blasphémera-t-il, l’ennemi insultera-t-il sans relâche à ton nom?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Pourquoi tiens-tu ta main à l’écart? Retire ta droite de ton sein! réduis -les à néant!
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Dieu est pourtant mon Roi depuis les temps antiques; il a accompli des œuvres de salut sur la terre.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
C’Est toi qui, par ta force, as fendu la mer, brisé la tête des monstres marins à la surface des eaux;
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
c’est toi qui as fracassé la tête du Léviathan, pour le donner comme pâture aux fauves du désert;
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
c’est toi qui as fait jaillir sources et torrents, mis à sec des fleuves puissants;
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
à toi appartient le jour, à toi aussi la nuit, c’est toi qui as créé l’astre lumineux, le soleil.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
C’Est toi qui as fixé toutes les limites de la terre, été et hiver sont ta création.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
N’Aie garde de l’oublier: l’ennemi blasphème, ô Eternel, un peuple méprisable insulte à ton nom.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Ne livre pas aux bêtes la vie de ta tourterelle, n’oublie pas à jamais l’existence de tes pauvres.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Tiens compte de l’alliance; car toutes les retraites cachées du pays sont devenues des repaires de violence.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Que l’opprimé ne soit pas acculé à la honte, que le pauvre et le nécessiteux puissent célébrer ton nom!
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Lève-toi, ô Dieu, défends ta cause, rappelle-toi les insultes qui, sans cesse, te viennent de gens indignes.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
N’Oublie pas les clameurs de tes adversaires, le tumulte toujours croissant de tes agresseurs.