< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
God, why have you abandoned/rejected us? Will you keep rejecting us forever [RHQ]? Why are you angry with us, since we are like sheep in your pasture [and you are like our shepherd]? [MET, RHQ]
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Do not forget your people whom you chose long ago, the people whom you freed [from being slaves in Egypt] and caused to become your tribe. Do not forget Jerusalem, which was (your home/where you dwelt) [on this earth].
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Walk along [and see] where everything has been totally ruined; our enemies have destroyed everything in the sacred temple.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Your enemies shouted triumphantly in this sacred place; they erected their banners [to show they had defeated us].
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
They cut down all the [engraved objects in the temple] like woodsmen cut down trees.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
Then they smashed all the carved wood with their axes and hammers.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
[Then] they burned your temple to the ground; they caused that place where you were worshiped to be unfit for people to worship in.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
They said to themselves, “We will destroy the Israelis completely,” and they [also] burned down all the other places where we gathered to worship God.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
All our sacred symbols (OR, miracles) are gone; there are no prophets now/any more, and no one knows how long [this situation will continue].
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
God, how long will our enemies make fun of you [RHQ]? Will they insult you [MTY] forever [RHQ]?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Why do you refuse to help [MTY, RHQ] us? Why do you keep your hand inside your cloak [instead of using it to destroy our enemies] [RHQ]?
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
God, you have been our king [all the time] since we came out of Egypt [HYP], and you have enabled us to defeat [our enemies] in the land [of Israel].
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
By your power you caused the [Red] Sea to divide; [it was as though] you smashed the heads of the [rulers of Egypt who were like] huge sea dragons [MET].
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
[It was as though] you crushed the head of the king of Egypt [MET] and gave his body to the animals in the desert to eat.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
You caused springs and streams to flow, and you [also] dried up rivers that had never dried up previously.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
You created the days and the nights, and you put the sun and the moon in their places.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
You determined where the oceans end and the land begins, and you created the summer/hot season and the winter/cold season.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Yahweh, do not forget that your enemies laugh at you, and that it is foolish people who despise you [MTY].
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Do not let your helpless people [MET] fall into the hands of their cruel enemies; do not forget your suffering/persecuted people.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Do not forget the agreement that you made with us; remember that there are violent people in every dark place on the earth.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Do not allow your oppressed people to be disgraced; help those poor and needy people in order that they will [again] praise you [MTY].
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
God, arise and defend yourself [by defending your people]! Do not forget that foolish people laugh at you (all day long/continually)!
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Do not forget that your enemies shout angrily [at you]; the uproar that they make [while they oppose you] never stops.

< Zabura 74 >