< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
A poem of Asaph why? O God have you rejected [us] to perpetuity does it smoke? anger your on [the] sheep of pasture your.
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Remember congregation your - [which] you acquired antiquity [which] you redeemed [the] tribe of inheritance your [the] mountain of Zion which - you have dwelt on it.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Lift up! footsteps your to [the] ruins of perpetuity everything he has done harm to [the] enemy in the sanctuary.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
They roared opposers your in [the] midst of appointed place your they set up signs their signs.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
It was known like [one who] brings upwards in a thicket of tree[s] axes.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
(And now *Q(K)*) engravings its altogether with axe[s] and crowbars they struck!
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
They sent in fire sanctuary your to the ground they profaned [the] dwelling place of name your.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
They said in heart their let us oppress them altogether they burned all [the] appointed places of God in the land.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Signs our not we have seen there not still [is] a prophet and not [is] with us [one who] knows until when?
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Until when? O God will he taunt [the] opponent will he spurn? [the] enemy name your to perpetuity.
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Why? do you draw back hand your and right [hand] your from [the] midst of (bosom your *Q(K)*) destroy.
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
And God [has been] king my from antiquity [who] does salvation in [the] midst of the earth.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
You you divided by strength your [the] sea you shattered [the] heads of sea monsters on the waters.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
You you crushed [the] heads of Leviathan you gave it food to a people to desert-dwellers.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
You you broke open a spring and a torrent you you dried up rivers of ever-flowing.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
[belongs] to You day also [belongs] to you night you you prepared a luminary and [the] sun.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
You you established all [the] boundaries of [the] earth summer and winter you you formed them.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Remember this [the] enemy he taunted - O Yahweh and a people foolish they spurned name your.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
May not you give to an animal [the] life of turtle-dove your [the] life of poor [people] your may not you forget to perpetuity.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Pay attention to the covenant for they are full [the] dark places of [the] land settlements of violence.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
May not he return [the] oppressed humiliated [the] poor and [the] needy may they praise name your.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Arise! O God conduct! case your remember reproach your from a fool all the day.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
May not you forget [the] sound of opposers your [the] uproar of [those who] rise against you [which] goes up continually.

< Zabura 74 >