< Zabura 74 >
1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
“A Maskil of Assaph.” Why, O God, hast thou cast us off for ever? why will thy anger smoke against the flock of thy pasture?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Remember thy congregation, which thou didst acquire of old; which thou didst redeem as the tribe of thy inheritance: this mount Zion, whereon thou hast dwelt.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Lift up thy steps unto the perpetual heaps of ruins: the enemy hath ill-used every thing in the sanctuary.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Thy adversaries have roared in the midst of thy places of assembly: they have set up their signs for signs.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
[The enemy] is known as one that lifteth up high axes against the thickets of a forest.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
And now they hew in pieces the carved work thereof altogether with hatchets and hammers.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
They have set on fire thy sanctuary; to the ground have they profaned the dwelling-place of thy name.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
They have said in their heart, We will oppress them altogether: they have burnt up all the places of assembly of God in the land.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Our signs do we not see: there is no more any prophet: and there is no one among us that knoweth how long.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
How long, O God, shall the adversary utter defiance? shall the enemy blaspheme thy name for ever?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Why withdrawest thou thy hand, and thy right hand? [draw it] out of thy bosom—exterminate [them];
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Since [thou] God art my King from olden days, working salvation in the midst of the earth.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
It was thou that didst divide by thy strength the sea: thou brokest in pieces the heads of the crocodiles on the waters.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Thou didst crush the heads of leviathan, and gavest them as food to the people inhabiting the wilderness.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Thou didst cleave fountain and stream: thou didst dry up ever-flowing rivers.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Thine is the day and thine is the night: it is thou who hast prepared the luminary and the sun.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
It is thou who hast set up all the boundaries of the earth: summer and winter—thou thyself hast formed them.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Remember this, that the enemy hath defied the Lord, and that a worthless foolish people have blasphemed thy name.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Oh give not up unto the multitude of enemies the soul of thy turtle-dove: the congregation of thy afflicted do not thou forget for ever.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Look unto the covenant; for the dark places of the earth are full of habitations of violence.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Oh let not the oppressed return confounded: let the poor and needy praise thy name.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Arise, O God, plead thy own cause: remember thy defiance from the worthless fool all the day.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Forget not the voice of thy adversaries: the tumult of those that rise up against thee ascendeth continually.