< Zabura 74 >
1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
A Psalme to give instruction, committed to Asaph. O God, why hast thou put vs away for euer? why is thy wrath kindled against the sheepe of thy pasture?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Thinke vpon thy Congregation, which thou hast possessed of olde, and on the rod of thine inheritance, which thou hast redeemed, and on this mount Zion, wherein thou hast dwelt.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Lift vp thy strokes, that thou mayest for euer destroy euery enemie that doeth euill to the Sanctuarie.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Thine aduersaries roare in the middes of thy Congregation, and set vp their banners for signes.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
He that lifted the axes vpon the thicke trees, was renowmed, as one, that brought a thing to perfection:
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
But nowe they breake downe the carued worke thereof with axes and hammers.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
They haue cast thy Sanctuarie into the fire, and rased it to the grounde, and haue defiled the dwelling place of thy Name.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
They saide in their hearts, Let vs destroy them altogether: they haue burnt all the Synagogues of God in the land.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
We see not our signes: there is not one Prophet more, nor any with vs that knoweth howe long.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
O God, howe long shall the aduersarie reproche thee? shall the enemie blaspheme thy Name for euer?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Why withdrawest thou thine hand, euen thy right hand? drawe it out of thy bosome, and consume them.
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Euen God is my King of olde, working saluation in the middes of the earth.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Thou didest deuide the sea by thy power: thou brakest the heads of the dragons in the waters.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Thou brakest the head of Liuiathan in pieces, and gauest him to be meate for the people in wildernesse.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Thou brakest vp the fountaine and riuer: thou dryedst vp mightie riuers.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
The day is thine, and the night is thine: thou hast prepared the light and the sunne.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Thou hast set all the borders of the earth: thou hast made summer and winter.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Remember this, that the enemie hath reproched the Lord, and the foolish people hath blasphemed thy Name.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Giue not the soule of thy turtle doue vnto the beast, and forget not the Congregation of thy poore for euer.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Consider thy couenant: for the darke places of the earth are full of the habitations of the cruell.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Oh let not the oppressed returne ashamed, but let the poore and needie prayse thy Name.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Arise, O God: mainteine thine owne cause: remember thy dayly reproche by the foolish man.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Forget not the voyce of thine enemies: for the tumult of them, that rise against thee, ascendeth continually.