< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
Zaburi ya Asafu. Hakika Mungu ni mwema kwa Israeli, kwa wale ambao mioyo yao ni safi.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
Bali kwangu mimi, miguu yangu ilikuwa karibu kuteleza; nilikuwa karibu mguu wangu kuachia uliposimama.
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
Kwa maana niliwaonea wivu wenye kujivuna nilipoona kufanikiwa kwa waovu.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
Wao hawana taabu, miili yao ina afya na nguvu.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
Hawapati shida zinazowataabisha watu wengine, wala hawapati mapigo kama wanadamu wengine.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Kwa hiyo kiburi ni mkufu wao, wamejivika jeuri.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Uovu hutoka katika mioyo yao iliyokufa ganzi, majivuno maovu kutoka mioyoni mwao hauna kikomo.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
Hudhihaki na kusema kwa ukorofi, katika majivuno yao wanatishia kutesa.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
Vinywa vyao huweka madai hata kwa mbingu, nazo ndimi zao humiliki duniani.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Kwa hiyo watu wao huwageukia na kunywa maji tele.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
Wanasema, “Mungu awezaje kujua? Je, Yeye Aliye Juu Sana anayo maarifa?”
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Hivi ndivyo walivyo waovu: siku zote hawajali, wanaongezeka katika utajiri.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Hakika nimeuweka moyo wangu safi bure, ni bure nimenawa mikono yangu nisiwe na hatia.
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
Mchana kutwa nimetaabika, nimeadhibiwa kila asubuhi.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
Kama ningesema, “Nitasema hivi,” ningelikuwa nimewasaliti watoto wako.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
Nilipojaribu kuelewa haya yote, yalikuwa magumu kwangu kuelewa.
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Mpaka nilipoingia patakatifu pa Mungu, ndipo nilipotambua mwisho wao.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Hakika unawaweka mahali pa utelezi, unawaangusha chini kwa uharibifu.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
Tazama jinsi wanavyoangamizwa ghafula, wanatoweshwa kabisa na vitisho!
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
Kama ndoto mtu aamkapo, hivyo wakati uinukapo, Ee Bwana, utawatowesha kama ndoto.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Wakati moyo wangu ulipohuzunishwa, na roho yangu ilipotiwa uchungu,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
nilikuwa mpumbavu na mjinga, nilikuwa mnyama mkatili mbele yako.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Hata hivyo niko pamoja nawe siku zote, umenishika mkono wangu wa kuume.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Unaniongoza kwa shauri lako, hatimaye utaniingiza katika utukufu.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Nani niliye naye mbinguni ila wewe? Dunia haina chochote ninachokitamani ila wewe.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Mwili na moyo wangu vyaweza kushindwa, bali Mungu ni nguvu ya moyo wangu na fungu langu milele.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Wale walio mbali nawe wataangamia, unawaangamiza wote wasio waaminifu kwako.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
Lakini kwangu mimi, ni vyema kuwa karibu na Mungu. Nimemfanya Bwana Mwenyezi kimbilio langu; nami nitayasimulia matendo yako yote.

< Zabura 73 >