< Zabura 73 >
1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
Та добар је Бог Израиљу, онима који су чиста срца.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
А ноге моје умало не зађоше, умало не попузнуше стопала моја,
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
Јер се расрдих на безумнике видећи како безбожници добро живе.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
Јер не знају за невољу до саме смрти, и тело је њихово претило.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
На пословима човечијим нема их, и не муче се с другим људима.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Тога ради опточени су охолоћу као огрлицом, и обучени у обест као у стајаће рухо.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Од дебљине избуљено им је око, срце пуно клапе.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
Подсмевају се, пакосно говоре о насиљу, охоло говоре.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
Уста своја дижу у небо, и земљу пролази језик њихов.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
И зато се онамо навраћају неки из народа његовог, и пију воду из пуног извора.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
И говоре: Како ће разабрати Бог? Зар Вишњи зна?
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Па ето, ови безбожници срећни на свету умножавају богатство.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Зар, дакле, узалуд чистим срце своје, и умивам безазленошћу руке своје,
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
Допадам рана сваки дан, и муке свако јутро?
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
Кад бих казао: Говорићу као и они, изневерио бих род синова Твојих.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
И тако стадох размишљати да бих ово разумео; али то беше тешко у очима мојим.
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Док најпосле не уђох у светињу Божију, и дознах крај њихов.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Та на клизавом месту поставио си их, и бацаш их у пропаст!
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
Како зачас пропадају, гину, нестаје их од ненадне страхоте!
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
Као сан, кад се човек пробуди, тако пробудивши их, Господе, у ништа обраћаш утвару њихову.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Кад кипљаше срце моје и растрзах се у себи,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
Тада бејах незналица и не разумевах; као живинче бијах пред Тобом.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Али сам свагда код Тебе, Ти ме држиш за десну руку.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
По својој вољи водиш ме, и после ћеш ме одвести у славу.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Кога имам на небу? И с Тобом ништа нећу на земљи.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Чезне за Тобом тело моје и срце моје; Бог је град срца мог и део мој довека.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Јер ево који одступише од Тебе, гину; Ти истребљаваш сваког који чини прељубу остављајући Тебе.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
А мени је добро бити близу Бога. На Господа полажем надање своје, и казиваћу сва чудеса Твоја.