< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
مزمور آساف هرآینه خدا برای اسرائیل نیکوست، یعنی برای آنانی که پاک دل هستند.۱
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
واما من نزدیک بود که پایهایم از راه در رود ونزدیک بود که قدمهایم بلغزد.۲
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
زیرا بر متکبران حسد بردم چون سلامتی شریران را دیدم.۳
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
زیراکه در موت ایشان قیدها نیست و قوت ایشان مستحکم است.۴
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
مثل مردم در زحمت نیستند ومثل آدمیان مبتلا نمی باشند.۵
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
بنابراین گردن ایشان به تکبر آراسته است وظلم مثل لباس ایشان را می‌پوشاند.۶
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
چشمان ایشان از فربهی بدر‌آمده است و از خیالات دل خود تجاوز می‌کنند.۷
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
استهزا می‌کنند و حرفهای بد می‌زنند و سخنان ظلم آمیز را از جای بلندمی گویند.۸
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
دهان خود را بر آسمانها گذارده‌اند وزبان ایشان در جهان گردش می‌کند.۹
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
پس قوم او بدینجا برمی گردند و آبهای فراوان، بدیشان نوشانیده می‌شود.۱۰
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
و ایشان می‌گویند: «خدا چگونه بداند و آیا حضرت اعلی علم دارد؟»۱۱
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
اینک اینان شریر هستند که همیشه مطمئن بوده، در دولتمندی افزوده می‌شوند.۱۲
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
یقین من دل خود را عبث طاهر ساخته و دستهای خود رابه پاکی شسته‌ام.۱۳
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
و من تمامی روز مبتلامی شوم و تادیب من هر بامداد حاضر است.۱۴
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
اگر می‌گفتم که چنین سخن گویم، هر آینه برطبقه فرزندان تو خیانت می‌کردم.۱۵
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
چون تفکرکردم که این را بفهمم، در نظر من دشوار آمد.۱۶
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
تابه قدسهای خدا داخل شدم. آنگاه در آخرت ایشان تامل کردم.۱۷
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
هر آینه ایشان را در جایهای لغزنده گذارده‌ای. ایشان را به خرابیها خواهی انداخت.۱۸
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
چگونه بغته به هلاکت رسیده‌اند! تباه شده، از ترسهای هولناک نیست گردیده‌اند.۱۹
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
مثل خواب کسی چون بیدار شد، ای خداوندهمچنین چون برخیزی، صورت ایشان را ناچیزخواهی شمرد.۲۰
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
لیکن دل من تلخ شده بود و در اندرون خود، دل ریش شده بودم.۲۱
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
و من وحشی بودم ومعرفت نداشتم و مثل بهایم نزد تو گردیدم.۲۲
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
ولی من دائم با تو هستم. تو دست راست مراتایید کرده‌ای.۲۳
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
موافق رای خود مرا هدایت خواهی نمود و بعد از این مرا به جلال خواهی رسانید.۲۴
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
کیست برای من در آسمان؟ و غیر ازتو هیچ‌چیز را در زمین نمی خواهم.۲۵
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
اگرچه جسد و دل من زائل گردد، لیکن صخره دلم وحصه من خداست تا ابدالاباد.۲۶
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
زیرا آنانی که ازتو دورند هلاک خواهند شد. و آنانی را که از توزنا می‌کنند، نابود خواهی ساخت.۲۷
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
و اما مرانیکوست که به خدا تقرب جویم. بر خداوندیهوه توکل کرده‌ام تا همه کارهای تو را بیان کنم.۲۸

< Zabura 73 >