< Zabura 73 >
1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
En salme av Asaf. Ja, Gud er god mot Israel, mot de rene av hjertet.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
Men jeg - nær hadde mine føtter snublet, på lite nær var mine trin glidd ut.
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
For jeg harmedes over de overmodige da jeg så at det gikk de ugudelige vel.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
For de er fri for lidelser inntil sin død, og deres styrke er vel ved makt.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
De kjenner ikke til nød som andre folk, og de blir ikke plaget som andre mennesker.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Derfor er overmot deres halssmykke, vold omhyller dem som et klædebon.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Deres øine står ut av fedme, hjertets tanker bryter frem.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
De håner og taler i ondskap om undertrykkelse; fra det høie taler de.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
De løfter sin munn op til himmelen, og deres tunge farer frem på jorden.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Derfor får de sitt folk til å vende sig om til dem, og vann i overflod suger de i sig.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
Og de sier: Hvorledes skulde Gud vite noget? Er det vel kunnskap hos den Høieste?
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Se, dette er de ugudelige, og evig trygge vokser de i velmakt.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Ja, forgjeves har jeg renset mitt hjerte og tvettet mine hender i uskyld;
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
jeg blev dog plaget hele dagen, og hver morgen kom til mig med tukt.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
Dersom jeg hadde sagt: Jeg vil tale således, se, da hadde jeg vært troløs mot dine barns slekt.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
Og jeg tenkte efter for å forstå dette; det var en plage i mine øine
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
- inntil jeg gikk inn i Guds helligdommer og gav akt på deres endelikt.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Ja, på glatte steder setter du dem; du lot dem falle, så de gikk til grunne.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
Hvor de blev ødelagt i et øieblikk! De gikk under og tok ende med forferdelse.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
Likesom en akter for intet en drøm når en har våknet op, således akter du, Herre, deres skyggebillede for intet når du våkner op.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Når mitt hjerte var bittert, og det stakk mig i mine nyrer,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
da var jeg ufornuftig og forstod intet; som et dyr var jeg imot dig.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Men jeg blir alltid hos dig, du har grepet min høire hånd.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Du leder mig ved ditt råd, og derefter optar du mig i herlighet.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Hvem har jeg ellers i himmelen? Og når jeg har dig, har jeg ikke lyst til noget på jorden.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Vansmekter enn mitt kjød og mitt hjerte, så er dog Gud mitt hjertes klippe og min del evindelig.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
For se, de som holder sig borte fra dig, går til grunne; du utrydder hver den som faller fra dig i hor.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
Men for mig er det godt å holde mig nær til Gud; jeg setter min lit til Herren, Israels Gud, for å fortelle alle dine gjerninger.