< Zabura 73 >
1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
Ein Psalm Asaphs. Nur gut ist Gott gegen Israel, gegen die, welche reinen Herzens sind.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
Ich aber hätte schier gestrauchelt mit meinen Füßen, wie leicht hätte ich einen Mißtritt getan!
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
Denn ich beneidete die Übermütigen, als ich den Frieden der Gottlosen sah.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
Denn sie leiden keine Qual bis zu ihrem Tod, und ihr Leib ist wohlgenährt.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
Sie werden nicht bemüht wie andere Leute und nicht geschlagen wie andere Menschen.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Darum schmücken sie sich stolz und kleiden sich frech.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Ihr Gesicht strotzt von Fett, sie bilden sich sehr viel ein.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
Sie reden höhnisch und boshaft, drohen mit höherer Gewalt.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
Sie reden, als käme es vom Himmel; ihre Worte haben Geltung auf Erden.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Darum wendet sich auch das Volk ihnen zu, und es wird von ihnen viel Wasser aufgesogen.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
Und sie sagen: «Was merkt Gott? Weiß der Höchste überhaupt etwas?»
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Siehe, das sind die Gottlosen; denen geht es immer gut, und sie werden reich!
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Ganz umsonst habe ich mein Herz rein erhalten und meine Hände in Unschuld gewaschen;
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
denn ich bin doch täglich geschlagen worden, und meine Strafe ist alle Morgen da!
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
Wollte ich auch so rechnen, siehe, so würde ich das Geschlecht deiner Kinder verraten.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
So sann ich denn nach, um dies zu verstehen; aber es schien mir vergebliche Mühe zu sein,
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
bis ich in das Heiligtum Gottes ging und auf ihr Ende merkte.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Nur auf schlüpfrigen Boden setzest du sie; du lässest sie fallen, daß sie in Trümmer sinken.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
Wie geschah das so plötzlich und entsetzlich! Sie gingen unter und nahmen ein Ende mit Schrecken.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
Wie einen Traum nach dem Erwachen, so wirst du, o Herr, wenn du dich aufmachst, ihr Bild verächtlich machen.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Als mein Herz verbittert war und es mir in den Nieren wehe tat,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
da war ich dumm und verstand nichts; ich benahm mich wie ein Vieh gegen dich.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Und doch bleibe ich stets bei dir; du hältst mich bei meiner rechten Hand.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Leite mich auch ferner nach deinem Rat und nimm mich hernach mit Ehren auf!
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Wen habe ich im Himmel? Und dir ziehe ich gar nichts auf Erden vor!
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Schwinden auch mein Fleisch und mein Herz dahin, so bleibt doch Gott ewiglich meines Herzens Fels und mein Teil.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Denn siehe, die fern von dir sind, kommen um; du vertilgst alle, die dir untreu werden.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
Mir aber ist die Nähe Gottes köstlich; ich habe Gott, den HERRN, zu meiner Zuflucht gemacht, um zu erzählen alle deine Werke.