< Zabura 73 >
1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
Psaume d’Assaph. Ah! Dieu est bon pour Israël, pour ceux qui ont le cœur pur.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
Pour moi, cependant, peu s’en faut que mes pieds n’aient bronché; pour un rien, mes pas auraient glissé.
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
Car je portais envie aux insensés: je voyais le bonheur des méchants.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
En effet, ils sont à l’abri de ces coups qui amènent la mort, et leur force demeure intacte.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
Ils n’ont pas leur part des misères humaines, ne subissent point les maux qui atteignent les autres.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Aussi sont-ils bouffis d’orgueil, et se drapent-ils dans leur violence comme dans un manteau.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Leurs yeux brillent à travers la graisse; les fantaisies de leur cœur dépassent toute borne.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
Ils ricanent et se targuent méchamment de tyrannie; ils parlent du haut de leur grandeur.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
Leur bouche s’attaque au ciel, leur langue promène ses ravages sur la terre.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
C’Est pourquoi son peuple en arrive au même point, et il absorbe de larges rasades d’eau,
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
tout en disant: "Comment le Tout-Puissant peut-il savoir? Le Dieu suprême possède-t-il la science?"
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Voyez ces méchants! Eternellement en sécurité, ils voient croître leur puissance.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
C’Est donc en vain que j’ai gardé mon cœur pur, et lavé mes mains pour qu’elles fussent sans tache:
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
je suis frappé sans relâche, ma peine se renouvelle chaque matin.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
Si je me fusse décidé à redire tout cela, certes j’aurais commis une trahison contre toute une génération de tes enfants.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
Je me mis donc à réfléchir pour comprendre la chose: ce fut une tâche pénible à mes yeux,
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
jusqu’à ce que, pénétrant dans le sanctuaire de Dieu, je me fusse rendu compte de leur fin.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Oui, tu les as mis sur un chemin glissant, tu les précipites dans la ruine.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
Oh! comme, en un instant, ils sont réduits à la désolation! Ils sont perdus, ils finissent dans l’épouvante.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
Comme un songe s’évanouit après le réveil, ainsi, Seigneur, quand tu te lèves, tu dissipes leurs vaines images.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Ainsi, quand mon cœur s’aigrissait et que mes reins étaient transpercés,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
j’étais un sot, ne sachant rien; j’étais comme une brute à ton égard.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Mais désormais je resterai toujours avec toi: tu as saisi ma main droite;
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
tu me guideras par ton conseil, et finalement tu me recueilleras avec honneur.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Qui donc aurais-je sans toi au ciel? A côté de toi, je ne désire rien sur terre.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Ma chair peut se dissoudre ainsi que mon cœur, Dieu sera à jamais le rocher de mon cœur et mon partage.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Certainement ils périront ceux qui s’éloignent de toi; tu anéantis tous ceux qui te deviennent infidèles.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
Pour moi, le voisinage de Dieu fait mon bonheur; j’ai mis ma confiance dans le Seigneur Dieu, prêt à proclamer toutes tes œuvres.