< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
A Psalm of Asaph. Truly God [is] good to Israel, [even] to such as are of a clean heart.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
But as for me, my feet were almost gone; my steps had well nigh slipped.
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
For I was envious at the foolish, [when] I saw the prosperity of the wicked.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
For [there are] no bands in their death: but their strength [is] firm.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
They [are] not in trouble [as other] men; neither are they afflicted like [other] men.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Therefore pride encompasseth them as a chain; violence covereth them [as] a garment.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Their eyes stand out with fatness: they have more than heart could wish.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
They are corrupt, and speak wickedly [concerning] oppression: they speak loftily.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
They set their mouth against the heavens, and their tongue walketh through the earth.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Therefore his people return hither: and waters of a full [cup] are wrung out to them.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
And they say, How doth God know? and is there knowledge in the Most High?
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Behold, these [are] the ungodly, who prosper in the world; they increase [in] riches.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Verily I have cleansed my heart [in] vain, and washed my hands in innocence.
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
For all the day long have I been afflicted, and chastened every morning.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
If I say, I will speak thus; behold, I should offend [against] the generation of thy children.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
When I thought to know this, it [was] too painful for me;
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Until I went into the sanctuary of God; [then] I understood their end.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Surely thou didst set them in slippery places: thou didst cast them down into destruction.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
How are they [brought] into desolation, as in a moment! they are utterly consumed with terrors.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
As a dream when [one] awaketh; [so], O LORD, when thou awakest, thou wilt despise their image.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Thus my heart was grieved, and I was pricked in my reins.
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
So foolish [was] I, and ignorant: I was [as] a beast before thee.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Nevertheless I [am] continually with thee: thou hast held [me] by my right hand.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Thou wilt guide me with thy counsel, and afterward receive me [to] glory.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Whom have I in heaven [but thee]? and [there is] none upon earth [that] I desire besides thee.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
My flesh and my heart faileth: [but] God [is] the strength of my heart, and my portion for ever.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
For lo, they that are far from thee shall perish: thou hast destroyed all them that go astray from thee.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
But [it is] good for me to draw near to God: I have put my trust in the Lord GOD, that I may declare all thy works.

< Zabura 73 >