< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
God truly is good to [us] Israeli people, to those who totally want to do all that God desires.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
As for me, I almost [stopped trusting in God]; [it was as though] my feet slipped and I stumbled [MET],
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
because I envied those who proudly [said that they did not need God], and I saw that they prospered [even though] they were wicked.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
Those people do not have any pains; they are [always] strong and healthy.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
They do not have the troubles/difficulties that other people have; they do not have problems like others do.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
So they are proud, and their being proud is [like] a necklace [that they show to others], and they show off their violent actions like people show off their beautiful robes.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
From their inner beings they (pour out/do) evil deeds, and they are always thinking about more evil things to do.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
They scoff at [other people], and they talk about doing evil things to them; they are proud while they plan to oppress others.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
They say evil things about [God who is in] heaven [MTY], and they talk boastfully/proudly about things [that they have done] here on the earth.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
The result is that people listen to what they say and praise them and do not think that they have done anything that is wrong.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
Wicked people say [to themselves], “God will certainly not [RHQ] know [what we have done]; [people say that] he is greater than any other god, but he does not know [everything].”
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
That is what wicked people are like; they never worry about anything, and they are always becoming richer.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
[So, God], I think it is useless that I have [RHQ] always done what you want me to, and that I have not sinned.
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
All day long I have problems, and every morning you punish me.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
If I had said the things that the wicked people say, I would have been sinning against your people.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
And when I tried to think about all this, it was very difficult for me [to understand it].
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
But when I went to your temple, [you spoke to me], and I understood what will happen to the wicked people [after they die].
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
[Now I know that] you will surely put them in slippery places, and they will fall down and die.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
They will be destroyed instantly; they will die in terrible ways.
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
They [will disappear as quickly] as a dream disappears when a person awakes in the morning; Lord, when you arise, you will (cause them to disappear/forget all about them).
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
When I felt sad/bitter, and brokenhearted,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
I was stupid and ignorant, and I behaved like an animal toward you.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
But I am always close to you, and you hold my hand.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
You guide me by teaching me, and (at the end [of my life]/when I die), you will receive me and honor me.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
You are in heaven and I belong to you [RHQ], and there is nothing on this earth that I desire more than that.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
My body and my mind may become very weak, but God, you continue to enable me to be strong; I belong to you forever.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Those who remain far from you will be destroyed; you will get rid of those who abandon you.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
But [as for] me, it is wonderful to be near to God and to be protected by Yahweh, and to proclaim to others all that he has done [for me].

< Zabura 73 >