< Zabura 73 >
1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
“BOOK III. A psalm of Asaph.” Truly God is good to Israel, —To those who are pure in heart.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
Yet my feet almost gave way; My steps had well nigh slipped:
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
For I was envious of the proud, When I saw the prosperity of the wicked.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
For they have no pains even to their death; Their bodies are in full health.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
They have not the woes of other men, Neither are they smitten like other men.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Therefore pride encircleth their neck as a collar; Violence covereth them as a garment.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
From their bosom issueth their iniquity; The designs of their hearts burst forth.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
They mock, and speak of malicious oppression; Their words are haughty;
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
They stretch forth their mouth to the heavens, And their tongue goeth through the earth;
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Therefore his people walk in their ways, And there drink from full fountains.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
And they say, “How doth God know? How can there be knowledge with the Most High?”
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Behold these are the ungodly! Yet they are ever prosperous; they heap up riches.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Verily I have cleansed my heart in vain; In vain have I washed my hands in innocence.
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
For every day have I been smitten; Every morn have I been chastened.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
If I should resolve to speak like them, Surely I should be treacherous to the family of thy children.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
So, when I studied to know this, It was painful to my eyes;
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Until I went into the sanctuaries of God, And considered what was their end.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Behold! thou hast set them on slippery places; Thou castest them down into unseen pits.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
How are they brought to desolation in a moment, And utterly consumed with sudden destruction!
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
As a dream when one awaketh, Thou, O Lord! when thou awakest, wilt make their vain show a derision.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
When my heart was vexed And I was pierced in my reins,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
Then was I stupid and without understanding; I was like one of the brutes before thee.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Yet am I ever under thy care; By my right hand thou dost hold me up.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Thou wilt guide me with thy counsel, And at last receive me in glory.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Whom have I in heaven but thee, And whom on earth do I love in comparison with thee?
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Though my flesh and my heart fail, God is the strength of my heart, and my portion for ever.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
For, lo! they who are far from thee perish; Thou destroyest all who estrange themselves from thee.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
But it is good for me to draw near to God; I put my trust in the Lord Jehovah, That I may declare all thy works.