< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
A Psalme committed to Asaph. Yet God is good to Israel: euen, to the pure in heart.
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
As for me, my feete were almost gone: my steps had well neere slipt.
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
For I feared at the foolish, when I sawe the prosperitie of the wicked.
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
For there are no bandes in their death, but they are lustie and strong.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
They are not in trouble as other men, neither are they plagued with other men.
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Therefore pride is as a chayne vnto them, and crueltie couereth them as a garment.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
Their eyes stande out for fatnesse: they haue more then heart can wish.
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
They are licentious, and speake wickedly of their oppression: they talke presumptuously.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
They set their mouth against heauen, and their tongue walketh through the earth.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Therefore his people turne hither: for waters of a full cup are wrung out to them.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
And they say, Howe doeth God know it? or is there knowledge in the most High?
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Lo, these are the wicked, yet prosper they alway, and increase in riches.
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Certainely I haue clensed mine heart in vaine, and washed mine hands in innocencie.
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
For dayly haue I bene punished, and chastened euery morning.
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
If I say, I will iudge thus, beholde the generation of thy children: I haue trespassed.
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
Then thought I to know this, but it was too painefull for me,
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Vntill I went into the Sanctuarie of God: then vnderstoode I their ende.
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Surely thou hast set them in slipperie places, and castest them downe into desolation.
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
How suddenly are they destroyed, perished and horribly consumed,
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
As a dreame when one awaketh! O Lord, when thou raisest vs vp, thou shalt make their image despised.
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Certainely mine heart was vexed, and I was pricked in my reines:
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
So foolish was I and ignorant: I was a beast before thee.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Yet I was alway with thee: thou hast holden me by my right hand.
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Thou wilt guide me by thy counsell, and afterward receiue me to glory.
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Whom haue I in heauen but thee? and I haue desired none in the earth with thee.
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
My flesh fayleth and mine heart also: but God is the strength of mine heart, and my portion for euer.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
For loe, they that withdrawe themselues from thee, shall perish: thou destroyest all them that goe a whoring from thee.
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
As for me, it is good for me to draw neere to God: therefore I haue put my trust in the Lord God, that I may declare all thy workes.

< Zabura 73 >