< Zabura 73 >

1 Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
Psalm van Asaf. Waarachtig; God is goed voor den rechtvaardige, Jahweh voor de reinen van hart!
2 Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
Toch waren haast mijn voeten gestruikeld, Mijn schreden bijna uitgegleden!
3 Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
Want ik was jaloers op de bozen, Omdat ik de voorspoed der zondaars zag;
4 Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
Voor hen toch bestaat er geen lijden, Gezond en vol kracht is hun lijf.
5 Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
Ze hebben geen zorgen als andere mensen, Worden niet als anderen geplaagd;
6 Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
Daarom hangen ze hoogmoed om als een keten, Bedekt hen geweld als een mantel.
7 Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
De misdaad puilt uit hun vet, Hun hart loopt over van slechte gedachten;
8 Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
Ze honen en lasteren, En dreigen op hoge toon met geweld.
9 Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
Ze zetten een mond op tegen de hemel, En hun tong gaat zich tegen de aarde te buiten.
10 Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
Daarom lopen de dwazen achter hen aan, En slurpen begerig hun woorden op.
11 Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
Ze zeggen: "Hoe zou God er iets van weten, De Allerhoogste er kennis van hebben?"
12 Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
Zie, zo gaat het de zondaars: Ze zijn altijd gelukkig, en hopen zich rijkdommen op!
13 Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
Heb ik dan mijn hart vergeefs in reinheid bewaard, En mijn handen in onschuld gewassen:
14 Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
De ganse dag word ik geplaagd, Iedere morgen opnieuw geslagen!
15 Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
Dacht ik: Zo wil ik spreken! Dan brak ik de trouw van het geslacht uwer kinderen;
16 Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
Maar als ik ging peinzen, om het te vatten, Dan bleef het een raadsel in mijn oog.
17 sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
Totdat ik in Gods raadsbesluiten drong, En op hun einde ging letten:
18 Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
Ja, Gij hebt ze op een glibberige bodem gezet, Ze gestort in hun eigen verderf!
19 Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
Hoe zijn ze in een oogwenk vernietigd, Verdwenen, in verschrikkelijke rampen vergaan:
20 Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
Heer, als een droom, die bij het ontwaken vervliegt, Wiens beeld we bij het opstaan verachten!
21 Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
Als dus mijn hart nog verbitterd zou zijn, En mijn nieren bleven geprikkeld,
22 na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
Dan was ik een dwaas en een zot, Een stuk vee in uw oog.
23 Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
Want ik blijf altijd bij U, Gij houdt mij bij de rechterhand;
24 Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
Gij leidt mij naar uw raadsbesluit, En herstelt mij in ere!
25 Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
Wat heb ik toch in de hemel; Ook op aarde verlang ik niets buiten U!
26 Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
Al bezwijken mijn vlees en mijn hart, God is voor eeuwig de Rots van mijn hart en mijn erfdeel.
27 Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
Maar die U verlaten, gaan zeker te gronde, Gij vernietigt wie van U afvalt;
28 Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.
Doch mij is het goed, in Gods nabijheid te blijven, En mijn vertrouwen te stellen op Jahweh, mijn Heer!

< Zabura 73 >