< Zabura 72 >
1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Süleyman'ın mezmuru Ey Tanrı, adaletini krala, Doğruluğunu kral oğluna armağan et.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Senin halkını doğrulukla, Mazlum kullarını adilce yargılasın!
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Dağlar, tepeler, Halka adilce gönenç getirsin!
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Mazlumlara hakkını versin, Yoksulların çocuklarını kurtarsın, Zalimleriyse ezsin!
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Güneş ve ay durdukça, Kral kuşaklar boyunca yaşasın;
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Yeni biçilmiş çayıra düşen yağmur gibi, Toprağı sulayan bereketli yağmurlar gibi olsun!
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Onun günlerinde doğruluk serpilip gelişsin, Ay ışıdığı sürece esenlik artsın!
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Egemenlik sürsün denizden denize, Fırat'tan yeryüzünün ucuna dek!
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Çöl kabileleri diz çöksün önünde, Düşmanları toz yalasın.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Tarşiş'in ve kıyı ülkelerinin kralları Ona haraç getirsin, Saba ve Seva kralları armağanlar sunsun!
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Bütün krallar önünde yere kapansın, Bütün uluslar ona kulluk etsin!
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Çünkü yardım isteyen yoksulu, Dayanağı olmayan düşkünü o kurtarır.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Yoksula, düşküne acır, Düşkünlerin canını kurtarır.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Baskıdan, zorbalıktan özgür kılar onları, Çünkü onun gözünde onların kanı değerlidir.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Yaşasın kral! Ona Saba altını versinler; Durmadan dua etsinler onun için, Gün boyu onu övsünler!
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Ülkede bol buğday olsun, Dağ başlarında dalgalansın! Başakları Lübnan gibi verimli olsun, Kent halkı ot gibi serpilip çoğalsın!
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Kralın adı sonsuza dek yaşasın, Güneş durdukça adı var olsun, Onun aracılığıyla insanlar kutsansın, Bütün uluslar “Ne mutlu ona” desin!
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
RAB Tanrı'ya, İsrail'in Tanrısı'na övgüler olsun, Harikalar yaratan yalnız O'dur.
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Yüce adına sonsuza dek övgüler olsun, Bütün yeryüzü O'nun yüceliğiyle dolsun! Amin! Amin!
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
İşay oğlu Davut'un duaları burada bitiyor.