< Zabura 72 >
1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Da al rey tu autoridad, oh Dios, y tu justicia al hijo del rey.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Puede ser un juez de su pueblo en justicia, y tomar decisiones verdaderas para los pobres.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Que las montañas den paz al pueblo y las colinas justicia.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Que él sea un juez de los pobres entre la gente, que pueda dar la salvación a los hijos de los necesitados; por él, deja que los violentos sean aplastados.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Que su vida continúe tanto como el sol y la luna, a través de todas las generaciones.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Que descienda como la lluvia sobre la hierba cortada; como lluvias que riegan la tierra.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
En sus días, a los rectos les irá bien, viviendo en paz mientras haya luna en el cielo.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Sea su reino de mar a mar, desde el río hasta los confines de la tierra.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Que los que están contra él desciendan delante de él; y que sus enemigos estén bajos en el polvo.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Vuelvan los reyes de Tarsis y de las islas con ofrendas; que los reyes de Saba y Seba entreguen sus dones.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Sí, que todos los reyes caigan delante de él; que todas las naciones sean sus siervos.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Porque él será un salvador para los pobres en respuesta a su clamor; y al que está en necesidad, sin un ayudante.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
El tendrá misericordia de los pobres, y será el salvador de los necesitados.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Él mantendrá sus almas libres de engaños y ataques violentos; y su sangre será de valor en sus ojos.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Que tenga vida larga, y que le sea entregado el oro de Saba; que se hagan oraciones por él en todo momento; bendiciones sean sobre él todos los días.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Hay campos de trigo que se extienden por la tierra, que tiemblan en la cima de las montañas, llenos de frutos como el Líbano; que sus tallos sean innumerables como la hierba de la tierra.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Que su nombre continúe para siempre, mientras el sol: que los hombres se bendigan por él; que todas las naciones bendigan su nombre.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Alabado sea el Señor Dios, el Dios de Israel, el único que hace maravillas.
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Alabado sea la gloria de su noble nombre para siempre; deja que toda la tierra se llene de su gloria. Entonces que así sea, que así sea.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Las oraciones de David, el hijo de Isaí, han terminado.