< Zabura 72 >
1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Oh ʼElohim, da tus juicios al rey, Y tu justicia al hijo del rey.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Él juzgará a tu pueblo con rectitud, Y a tus afligidos con justicia.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Que las montañas traigan paz al pueblo, Y las colinas, justicia.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Que Él defienda al afligido del pueblo, Que salve a los hijos del menesteroso, Y quebrante al opresor.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Que te teman mientras duren el sol y la luna, A través de todas las generaciones.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Que Él baje como lluvia sobre la hierba antes de cortarla, Como aguaceros que riegan la tierra.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Que en sus días florezcan los justos, Y abunde la paz hasta que no haya luna.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Que Él también domine de mar a mar, Y desde el río hasta los confines de la tierra.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Que ante Él se inclinen los nómadas del desierto, Y sus enemigos laman el polvo.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Que los reyes de Tarsis y las islas le traigan regalos. Que los reyes de Sabá y Seba le ofrezcan dones.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Que se postren ante Él todos los reyes, Y todas las naciones le sirvan.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Porque Él librará al necesitado que clama por ayuda, También al afligido y al que no tiene ayudador.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Tendrá compasión del pobre y necesitado, Y salvará las vidas de los menesterosos.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Rescatará sus vidas de opresión y violencia, Y la sangre de ellos será preciosa ante sus ojos.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
¡Que viva y se le dé el oro de Sabá! ¡Y que oren por él continuamente, Y que todo el día lo bendigan!
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Que haya abundancia de grano en la tierra, en la cima de las montañas. Que su fruto se agite como el Líbano, Y los de la ciudad florezcan como la hierba de la tierra.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
¡Que tu Nombre dure por siempre! Que tu Nombre sea propagado mientras brille el sol, Y que los hombres sean bendecidos por él. Que todas las naciones los llamen Inmensamente felices.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
¡Bendito sea Yavé ʼElohim, el ʼElohim de Israel, El único que hace maravillas!
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
¡Bendito para siempre sea tu Nombre glorioso, Y que toda la tierra sea llena de tu gloria! ¡Amén y amén!
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Terminaron las oraciones de David hijo de Isaí.