< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Para SalomãoDeus, dá teus juízos ao rei, e tua justiça ao filho do rei.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Ele julgará a teu povo com justiça, e a teus aflitos com juízo.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Os montes trarão paz ao povo, e os morros [trarão] justiça.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Ele julgará os pobres do povo, livrará os filhos do necessitado, e quebrará o opressor.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Temerão a ti enquanto durarem o sol e a luz, geração após geração.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Ele descerá como chuva sobre a [erva] cortada, como as chuvas que regam a terra.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Em seus dias o justo florescerá, e [haverá] abundância de paz, até que não [haja] mais a lua.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
E ele terá domínio de mar a mar; e desde o rio até os limites da terra.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Os moradores dos desertos se inclinarão perante sua presença, e seus inimigos lamberão o pó da terra.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Os reis de Társis e das ilhas trarão presentes; os reis de Sabá e Seba apresentarão bens.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
E todos os reis se inclinarão a ele; todas as nações o servirão;
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Porque ele livrará ao necessitado que clamar, e também ao aflito que não tem quem o ajude.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Ele será piedoso para o pobre e necessitado, e salvará as almas dos necessitados.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Ele livrará suas almas da falsidade e da violência, e o sangue deles lhe será precioso.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
E ele viverá; e lhe darão ouro de Sabá, e continuamente orarão por ele; o dia todo o bendirão.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Haverá bastante trigo na terra sobre os cumes dos montes; seu fruto brotará como o Líbano; e desde a cidade florescerão como a erva da terra.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Seu nome permanecerá para sempre; enquanto o sol durar, seu nome continuará; e se bendirão nele; todas as nações o chamarão de bem-aventurado.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Bendito [seja] o SENHOR Deus, o Deus de Israel! Somente ele faz [tais] maravilhas!
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
E bendito seja seu glorioso nome eternamente; e que sua glória encha toda a terra! Amem, e amém!
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
[Aqui] terminam as orações de Davi, filho de Jessé.

< Zabura 72 >