< Zabura 72 >
1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Av Salomo. Gud, gi kongen dine dommer og kongesønnen din rettferdighet!
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Han skal dømme ditt folk med rettferdighet og dine elendige med rett.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Fjellene skal bære fred for folket, og haugene for rettferdighets skyld.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Han skal dømme de elendige blandt folket, han skal frelse den fattiges barn og knuse voldsmannen.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
De skal frykte dig, så lenge solen er til, og så lenge månen skinner, fra slekt til slekt.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Han skal komme ned som regn på en nyslått eng, lik en regnskur, som væter jorden.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
I hans dager skal den rettferdige blomstre, og det skal være megen fred, inntil månen ikke er mere.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Og han skal herske fra hav til hav og fra elven inntil jordens ender.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
For hans åsyn skal de som bor i ørkenene, bøie kne, og hans fiender skal slikke støv.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Kongene fra Tarsis og øene skal komme med gaver, kongene fra Sjeba og Seba frembære skatt.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Alle konger skal falle ned for ham, alle hedninger skal tjene ham.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
For han skal frelse den fattige som roper, og den elendige som ingen hjelper har.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Han skal spare den ringe og fattige, og frelse de fattiges sjeler.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Han skal forløse deres sjel fra undertrykkelse og fra vold, og deres blod skal være dyrt i hans øine.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Og de skal leve og gi ham av Sjebas gull og alltid bede for ham; hele dagen skal de love ham.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Det skal bli overflod av korn i landet på fjellenes topp, dets frukt skal suse som Libanon, og det skal fremblomstre folk av byene som gresset på jorden.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Hans navn skal bli til evig tid; så lenge solen skinner, skal hans navn skyte friske skudd, og de skal velsigne sig ved ham; alle hedninger skal prise ham salig.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Lovet være Gud Herren, Israels Gud, han, den eneste som gjør undergjerninger!
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Og lovet være hans herlighets navn til evig tid, og all jorden bli full av hans herlighet! Amen, amen.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Ende på Davids, Isais sønns bønner.