< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Di Salomone. O Dio, da’ i tuoi giudizi al re, e la tua giustizia al figliuolo del re;
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
ed egli giudicherà il tuo popolo con giustizia, e i tuoi miseri con equità!
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
I monti produrranno pace al popolo, e i colli pure, mediante la giustizia!
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Egli farà ragione ai miseri del popolo, salverà i figliuoli del bisognoso, e fiaccherà l’oppressore!
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Ti temeranno fin che duri il sole, finché duri la luna, per ogni età!
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Ei scenderà come pioggia sul prato segato, come acquazzone che adacqua la terra.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Ai dì d’esso il giusto fiorirà, e vi sarà abbondanza di pace finché non vi sia più luna.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Egli signoreggerà da un mare all’altro, e dal fiume fino all’estremità della terra.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Davanti a lui s’inchineranno gli abitanti del deserto e i suoi nemici leccheranno la polvere.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
I re di Tarsis e le isole gli pagheranno il tributo, i re di Sceba e di Seba gli offriranno doni;
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
e tutti i re gli si prostreranno dinanzi, tutte le nazioni lo serviranno.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Poich’egli libererà il bisognoso che grida, e il misero che non ha chi l’aiuti.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Egli avrà compassione dell’infelice e del bisognoso, e salverà l’anima de’ poveri.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Egli redimerà l’anima loro dall’oppressione e dalla violenza, e il loro sangue sarà prezioso agli occhi suoi.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Egli vivrà; e a lui sarà dato dell’oro di Sceba, e la gente pregherà per lui tuttodì, lo benedirà del continuo.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Vi sarà abbondanza di grano nel paese, sulla sommità dei monti. Ondeggeranno le spighe come fanno gli alberi del Libano, e gli abitanti delle città fioriranno come l’erba della terra!
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Il suo nome durerà in eterno, il suo nome sarà perpetuato finché duri il sole; e gli uomini si benediranno a vicenda in lui; tutte le nazioni lo chiameranno beato!
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Sia benedetto l’Eterno Iddio, l’Iddio d’Israele, il quale solo fa maraviglie!
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Sia benedetto in eterno il suo nome glorioso, e tutta la terra sia ripiena della gloria! Amen! Amen!
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Qui finiscono le preghiere di Davide, figliuolo d’Isai.

< Zabura 72 >