< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Dari Salomo. Ya Allah, berikanlah hukum-Mu kepada raja dan keadilan-Mu kepada putera raja!
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Kiranya ia mengadili umat-Mu dengan keadilan dan orang-orang-Mu yang tertindas dengan hukum!
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Kiranya gunung-gunung membawa damai sejahtera bagi bangsa, dan bukit-bukit membawa kebenaran!
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Kiranya ia memberi keadilan kepada orang-orang yang tertindas dari bangsa itu, menolong orang-orang miskin, tetapi meremukkan pemeras-pemeras!
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Kiranya lanjut umurnya selama ada matahari, dan selama ada bulan, turun-temurun!
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Kiranya ia seperti hujan yang turun ke atas padang rumput, seperti dirus hujan yang menggenangi bumi!
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Kiranya keadilan berkembang dalam zamannya dan damai sejahtera berlimpah, sampai tidak ada lagi bulan!
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Kiranya ia memerintah dari laut ke laut, dari sungai Efrat sampai ke ujung bumi!
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Kiranya penghuni padang belantara berlutut di depannya, dan musuh-musuhnya menjilat debu;
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
kiranya raja-raja dari Tarsis dan pulau-pulau membawa persembahan-persemb kiranya raja-raja dari Syeba dan Seba menyampaikan upeti!
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Kiranya semua raja sujud menyembah kepadanya, dan segala bangsa menjadi hambanya!
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Sebab ia akan melepaskan orang miskin yang berteriak minta tolong, orang yang tertindas, dan orang yang tidak punya penolong;
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
ia akan sayang kepada orang lemah dan orang miskin, ia akan menyelamatkan nyawa orang miskin.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Ia akan menebus nyawa mereka dari penindasan dan kekerasan, darah mereka mahal di matanya.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
Hiduplah ia! Kiranya dipersembahkan kepadanya emas Syeba! Kiranya ia didoakan senantiasa, dan diberkati sepanjang hari!
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Biarlah tanaman gandum berlimpah-limpah di negeri, bergelombang di puncak pegunungan; biarlah buahnya mekar bagaikan Libanon, bulir-bulirnya berkembang bagaikan rumput di bumi.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
Biarlah namanya tetap selama-lamanya, kiranya namanya semakin dikenal selama ada matahari. Kiranya segala bangsa saling memberkati dengan namanya, dan menyebut dia berbahagia.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Terpujilah TUHAN, Allah Israel, yang melakukan perbuatan yang ajaib seorang diri!
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
Dan terpujilah kiranya nama-Nya yang mulia selama-lamanya, dan kiranya kemuliaan-Nya memenuhi seluruh bumi. Amin, ya amin.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Sekianlah doa-doa Daud bin Isai.

< Zabura 72 >