< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
E HAAWI i kou mau kanawai i ke alii, e ke Akua, A i kau pono hoi i ke keiki a ke alii.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
E hooponopono oia i kou poe kanaka ma ka pololei. A i kou poe haahaa ma ka pono.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
A e halihali mai no na mauna i ka pomaikai i kanaka, A me na puu liilii hoi, ma ka pono.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
E hooponopono oia i ka poe kaumaha o na kanaka, E hoola oia i na keiki a ka poe ilihune, E hana pepe i ka mea hooluhihewa.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
E weliweli mau lakou ia oe i ka wa o ka la, A i ka luli ana o ka mahina, i na hanauna a pau.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
E iho mai no ia e like me ka ua maluna o ka aina mauu i okiia; Me na kulu ua hoi i hoopulu iho i ka honua.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
E mohala ae ka poe pono i kona mau la, A me ka pomaikai nui a e ole loa ka mahina.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
E hoomalu aupuni oia mai ke kai a i ke kai, A mai ka muliwai hoi a i na welelau o ka honua.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
A imua o kona alo e kulou iho ai ko ka waonahele; A e palu no hoi kona poe enemi i ka lepo.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
E halihali mai na'lii o Taresisa a o na mokupuni i na makana; A e haawi mai no hoi na'lii o Seheba a me Seba i ko lakou mau haawina.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
Oia, e moe iho hoi na'lii a pau imua o kona alo; E pau hoi na lahuikanaka i ka malama ia ia.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
No ka mea, hoopakele no oia i ka mea waiwai ole i kona kahea ana; I ka mea ilihune hoi, a me ka mea nele i ke kokua ole.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
E hookoe mai no oia i ka mea haahaa, a me ka nele, A e hoola hoi i na uhane o ka poe hemahema.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
E hoopakele oia i ko lakou uhane i ka wahahee a me ka lalau wale: A he mea minamina ko lakou koko i kona mau maka.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
E ola no ia, a e haawiia nona ke gula no Seheba: E mau ana no ka pule nona; A e hoomaikai no ia i kela la i keia la.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
E nui auanei ka palaoa ma ka honua, ma ka piko o na mauna; A e luliluli kona hua e like me Lebanona: A e mohala ae ko ke kulanakauhale me he mauu la o ka honua.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
E mau ana no hoi kona inoa; E ulu no kona inoa, a e ole loa ka la: A e pomaikai na kanaka ia ia: E pau hoi na lahuikanaka i ke kapa aku ia ia he pomaikai.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
E hoomaikaiia o Iehova ke Akua, ko Iseraela Akua, Ka mea nana wale no i hana na mea kupaianaha.
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
E hoonani mau loa ia'ku kona inoa ihi, E hoopaapuia ka honua a pau i kona nani; Amene, a Amene.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Pau na pule a Davida ke keiki a Iese.

< Zabura 72 >